Iran ta buƙaci Qatar ta bari ta bincika ɓacewar direbobin jirginta uku a ƙasar
Rundunar sojin Iran ta ce ya kamata Qatar ta ba ta damar tura tawagar bincike domin gano abin da ya faru da matuƙan jiragen saman sojin Iran guda uku da suka ɓace.
Qatar ta musanta kwata-kwata cewa tana tsare da mutanen ukun, wadanda Tehran ta ce an harbo jiragen da suke tukawa a farkon yakin da ta yi da Amurka.
Wani kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Qatar ya ce an gano gawar daya daga cikin matukan, kuma an gayyaci Iran domin karbar ragowar gawar.
Wannan musantawar ta Qatar ta zo ne bayan wani janar din Iran, wanda ke jagorantar kwamitin sojin Iran mai neman mutanen da suka bace a yakin, ya yi zargin cewa an kama matukan jiragen ukun da ransu bayan jiragensu sun yi hatsari a watan Maris.