Majalisar Iran ta amince da ƙudirin daƙile tasirin ƙasashen waje a ƙasar

Asalin hoton, Getty Images
Majalisar dokokin Iran ta amince da ainihin tsarin wani kudiri da ake cewa zai taimaka wajen dakile tasirin hukumomin leƙen asiri, gwamnatoci da cibiyoyin ƙasashen waje a cikin ƙasar.
Kakakin majalisar, Abbas Goodarzi, ya ce an gabatar da ƙudirin ne domin kare Iran daga duk wani tasirin waje da ka iya shafar harkokin siyasa, tsaro da zamantakewa na ƙasar.
Tun a watan Yulin bara ne aka fara bayyana ƙudirin a gaban majalisar, sannan Kwamitin Tsaro da Harkokin Waje na majalisar ya amince da shi da rinjayen kuri'u a watan Oktoba.
Kakakin kwamitin, Ebrahim Rezaei, ya ce manufarsa ita ce ƙarfafa garkuwar Iran daga abin da ta ke kallon katsalandan daga ƙasashen waje.
Jami'an Jamhuriyar Iran sun sha bayyana damuwa a cikin shekarun baya kan abin da suke kira yunƙurin hukumomin leƙen asirin ƙasashen waje na yin tasiri a harkokin siyasa, zamantakewa da tsaro na ƙasar.
































