Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 05/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 5 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

  • Kwankwasiyya ta musanta fitar da Kwankwaso waje don neman lafiya
  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Nnamdi Kanu ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin ɗaurin rai-da-rai da aka yanke masa
  • An kashe ƴan Road Safety fiye da 100 a shekarar 2025 - Shugaban FRSC
  • An ceto mutane 166 da aka sace a Kajuru
  • Jami'an LASTMA sun ƙwace motoci 27 a Legas
  • Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta sake tura tawagar sa ido zuwa Tigray bayan ɓarkewar rikici
  • Musulmai 75 aka kashe a harin Kwara - AbdulRazaq
  • MDD ta yi gargaɗin barazanar nukiliya yayin da yarjejeniyar Amurka da Rasha ke ƙarewa
  • Tinubu ya tura bataliyar soji jihar Kwara

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Tinubu ya tura bataliyar soji jihar Kwara

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji zuwa sassan jihar Kwara, bayan mummunan harin da ya yi sanadiyyar kisan gomman mutane a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar.

    Shugaba Tinubu a wata sanarwa da kakakinsa Bayo Onanuga ya fitar ranar Laraba da dare ya kuma naɗa kwamandan da zai jagoranci rundunar sojin da za a tura jihar Kwara, wadda za ta gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya da aka yi wa laƙabi da 'Operation Savanna Shield'.

    Gwamnatin Najeriya ta ɗauki wannan mataki ne bayan harin da aka kai wa ƙauyen Woro, inda rahotanni ke cewa an tattara gawarwakin mutane 78 da maharan suka kashe.

    Hon Sa'idu Baba Ahmed, ɗan majalisar dokokin jihar Kwara ne, kuma ya shaidawa BBC cewa sun yi jana'izar sama da mutane 70 daga cikin waɗanda maharan suka kashe.

    Ya ce ''abin da dai na gani, waɗanda muka yi wa sallah, mutum 78 ne amma akwai waɗanda aka ƙone a cikin gidajensu, ba mu san adadin su ba tukun. An hallaka mutum zai kai 170.''

    Hon. Baba Ahmed ya kuma ce maharan ''sun wuce da mata 38,'' daga ƙauyukan da suka kai wa hari.

  2. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.