Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 1404/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 14/04/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Umar Mikail da Isiyaku Muhammed

  1. Rufewa

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin na BBC Hausa, da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, a nan za mu rufe shafin na yau Litinin, 14 ga watan Afirilu, 2025.

    A madadin kowa da kowa muke fatan za ku kasance da mu gobe, Talata in Allah Ya kai mu.

    Amma za ku iya ziyartar shafikanmu na sada zumunta da muhawara domin ci gaba da karanta labarai da kuma kallon bidiyo da muke sa muku, har ma ku tafka muhawara kan labaran.

    Mu rufe da wannan karin maganar da ke cewa - Kowa ya tuna wuyar noma ba zai yi kyautar dami ba

  2. Katangar makaranta ta kashe dalibai uku a Tunisia

    Wasu matasa dalibai uku sun mutu a Tunisia bayan da wata katanga a makarantarsu ta fada musu.

    Bayan wadanda suka rasun bangon ya kuma raunata wasu daliban biyu a babbar makarantar da ke yankin Sidi Bouzid na tsakiyar kasar ta Tunisia.

    An yada hotunan bidiyo da ke nuna jama'a na zanga-zanga a kan hadarin.

    Babbar kungiyar kwadago ta Tunisia ta yi kira da a yi zanga-zanga a makarantu a gobe Talata.

    Kungiyar ta bukaci a yi zanga-zangar cikin jimami da alhini da kuma nuna fushi kan gazawar gwamnati ta gyara gine-gine da sauran abubuwa na makarantun gwamnati.

  3. MDD ta ce sama da mutum dubu 60 girgizar kasa ta raba da muhallinsu a Myanmar

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce fiye da mutum dubu 60 ne suka rasa muhallansu a watan da ya gabata sakamakon girgizar kasa a Myanmar.

    Bayan amfani da wata na'ura, Majalisar ta ce an samu baraguzan gini da dama da manyan motoci 125 da aka tara daga gine-ginen da suka rushe abin da Majalisar ta ce akwai bukatar a kwashe su.

    Fiye da gine-ginen gidaje da ma'aikatun gwamnati dubu 10 ne suka rushe sakamakon girgizar kasar.

    Girgizar mai karfin maki 7 da digo 7 ta yi sanadin mutuwar mutum fiye da dubu uku inda ta bar mutane na tsugune, a wuraren da babu rufi saboda gidajensu duk sun rushe a cewar Majalisar.

  4. Dan-ci-ranin da ya janyo dambarwa tsakanin Amurka da El Salvador

    Shugaban El Salvador, ya ce ba zai mayar da mutumin nan da aka yi kuskuren mayar da shi kasarsa sannan aka daure shi a gidan yari a matsayin dandaba Amurka ba.

    Nayib Bukele, ya ce ba shi da ikon yin hakan.

    Shugaban ya fadi hakan ne yayin wata ganawa da Shugaba Trump a fadar gwamnatin Amurka.

    Sai dai kuma Shugaba Trump bai ce komai ba kan bayanin shugaban na El Salvador kan mayar da Kilmar Abrego Garcia Amurka.

    Fadar gwamnatin Amurka - White House, ta yarda cewa an mayar da Mista Abrego ne bisa kuskure.

  5. Masana sun gano hanyar rage yawan masu kamuwa da cutar ciwon zuciya

    Masana kimiyya sun ce wani sabon bincike ya nuna cewa bai wa masu fama da ciwon zuciya magunguna masu saukin kudi a farkon lokacin da aka tabbatar sun kamu da cutar zai taimaka wajen ceto dubban rayuka.

    Tawagar masanan da ta kunshi kwararru daga Birtaniya da kuma Sweden ta yi bincike a kan marassa lafiya 36.

    Masanan sun gano cewa bai wa mutanen da suka kamu da bugun zuciya magungunan rage kitse a cikin makonni 12 yana sa ana samun kyakkyawan sakamako.

    Tawagar masana kimiyyar ta ce a Birtaniya kadai, wannan mataki zai taimaka wajen rage samun akalla mutum dubu 5 daga kamuwa da bugun zuciya.

  6. Majalisar dokokin Hungary ta amince da takaita 'yancin masu neman jinsi daya

    Majalisar dokokin Hungary ta amince da wasu sauye-sauye na takaita 'yancin masu neman jinsi daya, a kundin tsarin mulkin kasar.

    Sauyin ya haramta taro ko gangamin masu neman jinsi daya a bainar jama'a - saboda kallon da ake wa taron a matsayin wata hanya ta yada dabi'ar luwadi da madigo da makamantan hakan.

    Matakin ya biyo bayan kudurin Firaministan kasar ta Hunagry Viktor Orban, wanda ya lashi takobin hana taron shekara-shekara na masu neman jinsi daya a babban birnin kasar, Budapest.

    An alakanta sauyin dokar taron ga dokokin kare yara, amma kuma masu kare 'yancin masu wannan dabi'a sun ce hakan nuna wariya da bambanci ne.

    Ana kallon wannan sauyin ga tsarin mulkin a matsayin mataki na baya-bayan nan na karfafa abin da Mista Orban ya kira, salon dumukuradiyyarsa maras walwala ko hana rayuwa ta sakaka.

  7. Firaministan Malaysia zai gana da shugaban mulkin sojin Myanmar don sulhu da 'yantawaye

    Firaministan Malaysia, ya ce zai gana da shugaban mulkin soji na Myanmar a makon nan domin neman a tsawaita yarjejeniyar dakatar da bude wuta a Myanmar din.

    A matsayinsa na shugaban kungiyar raya yankin (ASEAN), Anwar Ibrahim, ya ce ganawar tasa da Min Aung Hlaing za ta mayar da hankali wajen sake farfado da Myanmar daga mummunar girgizar kasar da ta afka mata a watan da ya gabata.

    Shekara hudu da ta wuce sojojin Myanmar suka kwace mulki, kuma tun daga wannan lokaci suke faman yaki da kungiyoyin tawaye daban-daban.

    A farkon watan Afirilu gwamnatin sojin ta amince da yarjejeniyar dakatar da bude wuta, amma kuma tuni Majalisar Dinkin Duniya ta ce, ta yi ta saba yarjejeniyar, abin da ya sa yake da wuya a raba kayan agaji.

  8. China ta gargadi Birtaniya kan siyasantar da harkar kasuwanci

    China ta gargadi Birtaniya da kada ta siyasantar da harkar kasuwanci, bayan da gwamnatin Birtaniyar ta zartar da wata dokar gaggawa, ta karbe iko da kamfanin China - British Steel, ranar Asabar.

    Ma'aikatar harkokin wajen China ta ce ya kamata a mutunta kamfanonin China da ke zuba jari da kuma aiki a Birtaniya, bisa adalci.

    Ministan Kudi na Birtaniya, James Murray, ya ce kasarsa za ta ci gaba da maraba da masu zuba jari na China - amma kuma tare da sanya ido sosai a kan harkokinsu.

    Kamfanin na British Steel da ke arewacin Ingila, ita ce ma'aikata ta karshe a Birtaniya da ke iya samar da karfe daga tama.

  9. Tsofaffin sojojin Isra'ila na neman kasar ta sake yarjejeniya da Hamas

    Sama da tsofaffin sojojin Isra'ila dubu 15 sun sanya hannu a wata sabuwar wasika suna kira ga gwamnatin kasar ta sake kulla yarjejeniyar sakin 'yan kasar da Hamas ta yi garkuwa da su a Gaza.

    A wasikar sun bukaci gwamnatin ta sake yarjejeniya da Hamas din ko da kuwa hakan na nufin kawo karshen yakin.

    Rokon ya biyo bayan irin wasikar da sojojin wucin-gadi na yanzu da kuma tsofaffi na kasar suka rubuta ne da kuma tsofaffin jami'an leken asiri na Isra'ilar.

    Sun bayyana matukar damuwarsu kan makomar sauran mutanen da Hamas ke rike da su tun bayan da Isra'ilar ta koma kai hari kan Hamas a fadin gaza a watan da ya wuce.

  10. PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

    Gwamnonin babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya sun nisanta kansu da yunƙurin haɗaka tsakanin jam'iyyarsu da wasu jam'iyyun siyasa.

    Ƙungiyar gwamnonin ƙarƙashin gwamnan Bauchi Bala Mohammed ta ce ba za ta haɗe da wata jam'iyya ba da nufin tunkarar zaɓen 2027.

    "Ba za mu shiga wata haɗaka ba da kowa da nufin tunkarar zaɓen 2027," kamar yadda ƙungiyar gwamnonin PDP ta bayyana a sanarwar da ta fitar bayan taron da suka gudanar a Ibadan jihar Oyo.

    Wannan dai ya ci karo da iƙirarin tsohon ɗantakarar jam'iyyar kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar a kwanakin baya inda ya ce suna yunƙurin ƙulla haɗaka da wasu jam'iyyu.

    Sanarwar gwamnonin PDP ta nuna akwai saɓanin ra'ayi tsakanin ɓangarensu da na Atiku Abubakar.

  11. 'Aƙalla mutum dubu 10 ne suka tsere wa cin zarafi a sansanin ƴan gudun hijira a Sudan'

    Ƙungiyar likitoci ta duniya ta MSF, ta ce sama da mutum dubu 10 ne suka tsere wa cin zarafi daga sansanin ƴan gudun hijira na Zamzam da ke Darfur zuwa garin Tawila, mai nisan kilomita sama da 70, a cikin kwana biyu da suka gabata.

    Sansanin da al'umma sama da rabin miliyan ke rayuwa sakamakon tsere wa yaƙi a wasu yankunan Darfur, ya kasance inda mayaƙan RSF ke kai wa hari tun a ƙarshen mako.

    Mayaƙan sun ce a yanzu suke iko da sansanin.

  12. 'Zulum ya kaɗu da bidiyon zane ɗalibi'

    Jami'an tsaro a jihar Borno sun kama wani malami da ake zargi da cin zarafin wani ƙaramin yaro ta hanyar zane shi, wanda aka gani cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta.

    Bidiyon, mai tayar da hankali, ya nuna yadda malamin ke dukan ɗan ƙaramnin yaron da sanda yayin da wani yaron kuma ke watsa masa ruwa da kasa a jikinsa cikin zafin rana.

    Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce yara 6 cikin 10 na fuskantar wani nau’i na cin zarafi a Najeriya.

    Mai magana da yawun gwamnan jihar Borno, Dauda Iliya ya bayyana wa BBC cewa lamarin ya ɗaga hankalin Gwamnan jihar, Babagana Zulum, wanda hakan ya sa gwamnan ya bayar da umarnin a nemo malamin.

    Sai dai ya ce tun a lokacin azumi ne lamarin ya faru, "amma sai yanzu ya fito ya karaɗe shafukan sada zumunta. Gwamna ya kaɗu matuƙa. Shi ya sa ya bayar da umarnin a nemo mutumin, wanda malamin yaron ne. Yanzu an kama shi, an miƙa shi ga jami'an tsaro."

    Dauda Iliya ya ƙara da cewa gwamnan ya sa an kawo masa yaron, kuma ya ce a kawo masa mahaifiyarsa.

    "Mahaifiyar tana zaune ne a Munguno, Boko Haram sun kashe mahaifinsa. Amma yanzu gwamna ya saya musu gida a cikin Maiduguri, sannan zai ɗauki nauyin karatunsa."

  13. Kongo: Ƙasa mai ɗimbin arziƙi wadda talauci ya yi wa katutu

    Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ƙasa ce mai ƙunshe da ɗimbin albarkatun ƙasa masu tsada a ƙarƙashinta, waɗanda ake amfani da su wajen haɗa wayoyin salula da kuma motoci masu amfani da lantarki.

    Sai dai duk da irin wannan arziƙi da take da shi, ƙasar ta kasance cikin mafiya talauci kuma mafi fama da rikice-rikice a fadin duniya.

  14. Zelensky ya gayyaci Trump zuwa Ukraine kafin yarjejeniya da Rasha

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya gayyaci Shugaban Amurka Donald Trump domin ziyartar ƙasarsa kafin ya shiga yarjejeniyar tsagaita wuta da Rasha.

    "Kafin ɗaukar kowane irin mataki, ko shiga yarjejeniya, ina so ka zo ka ga halin da mutanenmu suke ciki, halin da fararen hula da dakaru suke ciki, ka ga yadda aka lalata asibitoci da makarantun ƙasar," in ji Zelensky a tattaunawarssa da shirin minti 60 na CBS.

    An naɗi tattaunawar ne kafin Rasha ta harba wani makami mai linzami a birnin Sumy, wanda ya kashe aƙalla mutum 34, sannan ya jikkata aƙalla 117.

    Sai dai Rasha ta ce tana kai hare-haren ne kan sojoji ko kuma masu alaƙa da mayaƙa, amma Trump ya ce an faɗa masa cewa hare-haren kuskure ne.

  15. Ƴan Nijar mazauna Libya sun buƙaci gwamnatin Tchiani ta kai musu ɗauki

    Ƴan Nijar mazauna ƙasar Libiya sun koka kan mawuyacin halin da suke ciki a sakamakon wani gagarumin kamen ƴan Nijar da hukumomin ƙasar ta Libiya suka ƙaddamar kan ƴan Nijar.

    Yanzu haka dai shaidu daga ƙasar ta Libiya sun bayyana cewa akwai ɗaruruwan ƴan Nijar da aka kama a kamen na bayan nan inda ake tsare da su a gidajen kurkuku dabam-dabam na ƙasar.

    Ƴan Nijar ɗin na kokawa ne kan yadda kamen ya shafi hatta masu takardun zama da kuma yadda jami'an ke ƙwace masu dukiya da kwashe masu kadarori a wuraren zamansu.

    Wasu daga cikin ƴan Nijar ɗin a ƙasar ta Libiya sun yi kira ga gwamnatin Tchiani da ta gaggauta saka bakinta a cikin lamarin domin ganin hukumomin ƙasar ta Libiya sun sako ƴan Nijar ɗin da aka kama a lokacin samamen wanda yanzu haka ake ci gaba da shi.

  16. Tarayyar Turai za ta tallafa wa gwamnatin Falasɗinawa da dala biliyan 1.8

    Tarayyar Turai ta sanar da yunƙurinta na ba gwamnatin Falasɗinawa tallafin kuɗi dala biliyan biliyan 1.8 wanda za a tura mata a cikin shekara uku.

    Kwamishinan tarayyar a yankin, Dubravka Šuic, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa tallafin, wanda wani ɓangarensa zai zama kamar bashi ne, zai taimaka wajen ba gwamnatin yankin damar inganta shugabancinta, bayan zargin da take sha na mulki mara kyau.

    Rahotanni sun ce tarayyar na fatan shugabannin yankin za su iya ɗaukar nauyin kula da yankin Gaza a nan gaba.

    Amma gwamnatin Isra'ila ta yi watsi da matakin, musamman yunƙurin samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kansu, wanda ke nufin Falasɗinu za ta zama ƴantacciyar ƙasa.

  17. An yi garkuwa da ƴar Swizerland a Nijar

    A jihar Agadez ta jamhuriyar Nijar wasu mutane ne da ba a san ko su wane ne ba, sun yi garkuwa da Ms. Claudia, ƴar ƙasar Switzerland a daren ranar Lahadi 13 ga Afrilu a tsakanin ƙarfe 8 zuwa ƙarfe 10 na dare.

    An yi garkuwa da ita ne a gidanta da ke unguwar Dagmanet 2 a Agadez.

    Claudia, haifaffiyar ƙasar Lebanon, ta zauna a Agadez shekaru da dama da suka gabata bayan zamanta a Aljeriya inda ta yi aikin yawon buɗe ido.

    Claudia ta auri wani ɗan Nijar, ta ƙaddamar da wata ƙungiya a Agadez don ba da taimako ga masu sana'a.

    A baya-bayan nan ma an samu irin haka, inda wasu mahara suka yi garkuwa wata ƴar Austriya Eva Gretzmacher a ranar 11 ga Janairu, 2025.

  18. ‘Na shafe shekara 30 ina aikin gyaran titi kyauta a Najeriya’

    Daniel Dabo yana aikin gyaran titi na ne sa-kai a Abuja da Nasarawa tun shekarun 1900 domin sauƙaƙa wa masu ababen hawa yi tafiya.

    Masu tafiya a kan titi sun bayyana cewa Daniel mutum mai ƙwazo, wanda yake aikin gyaran titi a kowane yanayi, ko da a cikin ruwan sama ne ko zafin rana.

    "Idan na ga hanya ta lalace, ina gyarawa ba tare da an faɗa min ba"

  19. Algeria za ta kori ma'aikatan ofishin jakadancin Faransa 12 daga ƙasar

    Algeria ta kori ma'aikatan ofishin jakadancin Faransa guda 12, inda hukumomin ƙasar suka buƙace su da su fice daga ƙasar nan da awa 48, kamar yadda ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noel Barrot ya bayyana.

    Ministan ya ce lamarin ba zai rasa nasaba da samun ƴan Algeria uku da laifin a Faransa ba, ciki har da wani ma'aikacin ofishin jakadanci.

    An kama su ne bisa zarginsu da hannu a garkuwa da wani mai suna Amir Baokhors mai shekara 41, mai ɗimbin mabiya a kafofin sadarwa na zamani, wanda yake sukar gwamnatin Algeria.

    Baokhors yana zaman mafaka ne a Faransa bayan ya tsere daga ƙasar ta Algeria.

    Barrot ya yi kira ga Algeria da ta dakatar da yunƙurinta na sallamar ma'aikatan, inda ya ce Faransa za ta "ɗauki mataki" idan suka aiwatar da lamarin.

  20. Likitocin Gaza na cikin mawuyacin hali - WHO

    Wata mai magana da yawun Hukumar Lafiya ta Duniya ta shaida wa BBC cewa yanayin da likitocin da ke asibitocin Gaza ke ciki sun wuce a misaltawa.

    Margaret Harris tana magana ne bayan da wani likita a asibitin Al-Ahli ya ce makamai masu linzami na Isra'ila sun lalata sashen bayar da kulawa ta musamman na asibitin.

    Isra'ila ta ce ta kai harin ne kan wata cibiyar Hamas amma ba ta bayar da hujja ba.

    Ms Harris ke nan take cewa cibiyoyin kula da lafiya na da kariya a karƙashin dokokin jin ƙai na ƙasa da ƙasa, a bayyana take ƙarara bai kamata a kai wa cibiyoyin kula da lafiya hari ba.

    Ta ce likitocin Gaza na gwagwarmayar yi wa gomman mutanen da suka ji rauni tiyata sakamakon luguden wutar na Isra'ila.