Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 19/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 19 ga watan Agusta, 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello, Haruna Kakangi da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Har yanzu ba a saki dukiyoyinmu da aka riƙe ba - Shugaban Babban Bankin Iran

    Shugaban Babban Bankin Iran, Abdolnaser Hemmati, ya ce kawo yanzu ba a saki ko ɗaya daga cikin kuɗaɗe da kadarorin Iran da aka rike musu ba, kamar yadda aka tanada a yarjejeniyar fahimtar juna ta Islamabad.

    A wata hira da gidan talabijin, Hemmati ya bayyana rahotannin cewa an mayar wa Iran wasu kuɗaɗe da zinare a matsayin jita-jita.

    Ya ce har yanzu babu wata kadara ko kuɗin Iran da aka saki bisa yarjejeniyar.

    A ƙarƙashin sashe na 11 na yarjejeniyar, Amurka ta yi alƙawarin bai wa Iran cikakkiyar damar amfani da kadarorinta da aka riƙe, tare da bayar da lasisin da ake buƙata domin mayar da kuɗin zuwa asusun da Babban Bankin Iran ya amince da su.

    Sai dai wani jami’in Amurka ya ce sakin wasu daga cikin kadarorin zai dogara ne kan cika alkawarin da Iran ta ɗauka, ciki har da bayar da haɗin kai kan batun shirinta na nukiliya.

  2. Shugaban sojojin Isra’ila ya ziyarci yankunan da ta mamaye a Syria

    Shugaban hafsoshin sojojin Isra’ila, Eyal Zamir, ya ce Isra’ila ba za ta bari wata barazana ta samu gindin zama kusa da iyakokinta ba.

    Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake ziyartar wani yankin tsaro da Isra’ila ta mamaye a kudancin Syria.

    Ya ce Isra’ila ba za ta janye daga shirin ko shirin ko-ta-kwana na sojojinta a kowane daga cikin wuraren da ake gwabza yaƙi ba, ciki har da Syria.

    Sojojin Isra’ila sun kasance a yankin tun bayan kifar da gwamnatin Bashar al-Assad a watan Disamban 2024.

    Ziyarar Zamir ta zo ne kwana guda bayan da Isra’ila ta kai hari kan sansanin sojin sama na Abu Dhuhr da ke lardin Idlib a arewa maso yammacin Syria.

  3. Za a iya sake tattaunawa da Iran, amma abubuwa suna tafiya yadda ya kamata - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce akwai yiwuwar Amurka ta sake tattaunawa da Iran a wani lokaci, amma ya ce a halin yanzu abubuwa suna tafiya “sosai”.

    Trump ya ce duk wata tattaunawa da Iran za ta dogara ne kan ta yi watsi gaba ɗaya da ƙoƙarinta na mallakar makaman nukiliya.

    Ya kuma jaddada cewa ba zai bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba, saboda a cewarsa, za ta yi amfani da shi.

    Shugaban na Amurka ya kuma ce dakarun ƙasarsa suna da “cikakken iko” kan Mashigar Hormuz, inda ya ce jiragen ruwa da dama sun ratsa mashigar a daren jiya.

    Ya ce duk da cewa hare-haren jirage marasa matuƙa na ci gaba lokaci zuwa lokaci, galibinsu sun wuce “ba wata matsala” ba.

    Trump ya ce farashin man fetur ya kai tsakanin dala 83 zuwa 85 a ganga, amma zai ragu sosai bayan kawo ƙarshen rikicin.

  4. Isra'ila ta kashe mutum 9 a wani hari kan ofishin ƴansanda a Gaza

    Likitoci a Gaza sun ce aƙalla mutum tara ne aka kashe, yayin da wasu 15 suka jikkata a wani hari da Isra’ila ta kai kan ofishin ƴansanda a Gaza.

    Majiyoyin sun ce wasu daga cikin waɗanda aka kashe manyan jami’an ƴansanda ne.

    Baya ga haka wani mutum ɗaya ya mutu a yau a wani harin Isra’ila kan sansanin ƴan gudun hijirar Nuseirat da ke tsakiyar Gaza.

    Majiyoyin sun kuma ce mutum bakwai, ciki har da wani yaro, sun mutu a wani harin Isra’ila kan wani wurin cin abinci da ke bakin teku ranar Talata.

    Ƙaruwar hare-haren na zuwa ne bayan ziyarar da wakilin Amurka Jared Kushner ya kai yankin, wadda ta gaza samar da ci gaba wajen aiwatar da shirin da aka tsara.

  5. Manyan jiragen dakon mai biyu na China sun maƙale a Mashigar Hormuz

    Rahotanni sun ce wasu manyan jiragen dakon ɗanyen mai biyu na China sun tsallaka Mashigar Hormuz, amma daga bisani sun kasa ci gaba da tafiyarsu kuma sun makale a yankin.

    Ɗaya daga cikin jiragen, Sea V, ya ɗauko ɗanyen mai daga Iraki a ranar Talata kafin ya nufi Mashigar Hormuz.

    Sai dai daga baya ya juya, inda yanzu yake maƙale a mashigar.

    Jirgin na ɗauke da tutar Hong Kong, kuma bayanan sa ido kan jiragen ruwa sun nuna cewa wani kamfani na China ne ya mallake shi.

    Jirgin na biyu, Hestia, wanda shi ma ke ɗauke da tutar Hong Kong, ya isa Tekun Farisa a farkon makon nan, ya shiga Mashigar Hormuz kafin daga baya ya sauya hanya zuwa Tekun Oman.

    Rahotanni sun ce dukkan ma'aikatan jirgin 'yan China ne.

    Wannan na zuwa ne yayin da manyan kamfanonin jigilar kaya na China suka dakatar da tura jiragen dakon mai ta Mashigar Hormuz da Bab al-Mandab saboda ƙarin haɗarin hare-haren jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami.

  6. Tinubu ya naɗa Abel Olumuyiwa sabon shugaban ma’aikatan tarayya

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Abel Olumuyiwa Enitan a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Tarayyar ƙasar, inda zai fara aiki daga ranar 27 ga Agustan 2026.

    Enitan zai maye gurbin Didi Esther Walson-Jack, wadda za ta yi ritaya daga aikin gwamnati bayan ta kai shekarun ritaya na doka, wato shekaru 60.

    Enitan ɗan asalin Jihar Osun ne kuma shi ne babban sakataren ma’aikatar tarayya mafi girma a yanzu. Ya shafe shekaru bakwai da watanni bakwai yana matsayin babban sakatare, inda ya yi aiki a Ma’aikatar Harkokin ’Yan Sanda, Ma’aikatar Jin Kai da kuma Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa.

    A yanzu yana matsayin babban sakatare a Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya.

    Fadar Shugaban Ƙasar ta ce Enitan na da kwarewa sosai kan tsarin aikin gwamnatin tarayya, kuma Tinubu ya umarce shi da ya ci gaba da inganta sauye-sauyen da ake yi a ma’aikatun gwamnati, tare da ƙara nuna ƙwarewa, gaskiya da adalci wajen gudanar da ayyuka.

    Sanarwar da Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaba Tinubu ya fitar ta ce an haifi Enitan a ranar 12 ga Disamban 1966. Ya yi karatun digiri a fannin kuɗi da harkokin banki a Jami’ar jihar Legas, kuma ya samu digiri na biyu a fannin Nazarin Manufofin Gwamnati daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Lafia.

  7. Kusan utum 30 sun mutu a ruftawar mahakar zinare a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

    Akalla masu hakar zinare 30 ne suka mutu bayan ruftawar wata mahakar zinare a yammacin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, kusa da iyakar ƙasar Kamaru. Lamarin ya faru ne ranar Talata a yankin Abba na lardin Nana-Mambéré.

    Mahakar ta rufta ne yayin da ake aikin hakar zinare, inda aka binne wasu masu aikin a ƙarƙashin kasa. Ana ci gaba da aikin ceto domin neman waɗanda ake kyautata zaton suna makale a wurin, yayin da wasu daga cikin waɗanda suka jikkata ke samun magani.

    Hotunan da aka dauka a wurin sun nuna masu aikin ceto suna ƙoƙarin fitar da gawawwaki daga mahakar, yayin da ake ci gaba da fargabar cewa adadin waɗanda suka mutu zai iya ƙaruwa. Har yanzu ba a bayyana abin da ya haddasa ruftawar ba.

  8. Shugaban Ukraine ya kori mataimakiyar shugaban fadar shugaban ƙasar

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya kori mataimakiyar shugaban fadar shugaban ƙasar, Iryna Mudra, bayan jami'an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasar sun kai samame a ofishinta. An kuma binciki wuraren wasu 'yan majalisa da jami'an gwamnati.

    Hukumar ta ce binciken yana da alaƙa da wani zargin karkatar da kusan dala miliyan uku domin biyan belin tsohon Ministan Makamashi, Herman Halushchenko. Hukumar na binciken asalin kuɗin belin da kamfanoni huɗu suka biya.

    Samamen ya zo ne kwana guda bayan tsohon Ministan Tsaron Ukraine, Mykhailo Fedorov, ya yi kira da a gudanar da zaɓe a ƙasar duk da ci gaba da yaƙi da Rasha. A karkashin dokar taƙaita wasu 'yanci da aka kafa saboda yaƙin, ba a gudanar da zaɓe a Ukraine a halin yanzu.

  9. Me yarjejeniyar zaman lafiya da jam'iyyu suka sanya wa hannu ta ƙunsa?

    A ranar Talatya ne manyan jam'iyyun siyasa da ƴan takararsu suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya (Peace Accord) a Abuja, inda suka yi alƙawarin gudanar da yaƙin neman zaɓen cikin lumana da mutunta dokokin zaɓe.

    Taron sanya hannu kan yarjejeniyar, wanda Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban mulkin soja Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya ya shirya, ya samu halartar wakilan gwamnati da shugabannin jam'iyyun siyasa da ƴan takarar shugaban ƙasa da shugaban hukumar zaɓe ta INEC da jami'an tsaro da kuma jakadun ƙasashen waje.

    Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume, yayin da ƴan takara irin su Peter Obi da Omoyele Sowore suka halarta tare da sanya hannu a yarjejeniyar.

    To ko me yarjejeniyar ta ƙunsa, kuma ta yaya za ta taimaka don tabbatar da gudanar da zaɓen cikin lumana? Waɗannan ne tambayoyin da mutane da dama ke yi game da batun.

  10. Babban ɗan takarar adawa a Zambia zai kalubalanci sakamakon zaɓen ƙasar a Kotu

    Babban ɗan takarar adawa a Zambia, Brian Mundubile, ya ce zai kalubalanci nasarar Shugaba Hakainde Hichilema a gaban kotu, yana zargin an tafka magudi a zaɓen da aka gudanar a makon da ya gabata.

    Hukumar zaɓen ƙasar ta ayyana Hichilema a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kusan kashi 60 cikin 100 na ƙuri'un da aka kada, yayin da Mundubile ya samu kusan kashi 38 cikin 100.

    A gefe guda, babban jami'in Majalisar Ɗinkin Duniya mai kula da haƙƙin ɗan'adam ya nuna damuwa kan kama da tsare 'yan adawa a lokacin zaɓen, tare da kira ga hukumomin Zambia da su tabbatar da mutunta dokoki da haƙƙin waɗanda aka kama.

    Jam'iyyar Mundubile ta ce a yanzu yana wani wuri mai tsaro ƙarƙashin kariyar wata ƙungiyar kare haƙƙin ɗan'adam ta ƙasa da ƙasa, bayan wata arangama da jami'an tsaro a ranar zaɓe. Mundubile ya musanta zargin hukumomi cewa an samu makamai a wurin da yake.

  11. A shirye muke mu tunkari duk wata barazana daga Iran — NATO

    Ƙungiyar tsaro ta NATO ta ce a shirye take ta tunkari duk wata barazana daga Iran, kuma za ta ɗauki matakan da suka dace a ko da yaushe domin kare ƙasashe mambobinta.

    Wani jami'in ƙungiyar ne ya bayyana hakan yayin da yake maida martani kan wani rahoton jaridar Financial Times da ya ce Iran na iya kai hari kan sansanonin sojojin Amurka a Turai idan Donald Trump ya ƙara tsananta yaƙin.

    Jami'in NATO ya ce: “Tsarinmu na dakile barazana da kare kai yana da ƙarfi kuma yana aiki yadda ya kamata, kamar yadda aka gani a farkon wannan shekarar lokacin da tsarin tsaron sararin samaniyar NATO ya yi nasarar tare makamai masu linzami da Iran ta harba zuwa Turkiyya a lokuta huɗu daban-daban.”

    Jaridar Financial Times, wadda ta rawaito wasu mutane da ke da kusanci da gwamnatin Iran, ta ce Iran tana nazarin kai hari kan wuraren sojojin Amurka a Turai idan Trump ya ƙara tsananta yaƙin, yayin da “Tehran ke nazarin hanyoyin da za ta ƙara tsananta rikicin.”

    Jaridar ta kuma rawaito wasu majiyoyi biyu da ke da masaniya kan gwamnatin Iran cewa sojojin Iran sun tantance kadarorin Amurka da ke wasu ƙasashen kudu maso gabashin Turai, ciki har da Bulgaria, wadda a watan da ya gabata ta ba da izinin amfani da sansanin sojinta wajen ɗaukar mai ga jiragen saman Amurka.

  12. Isra'ila za ta yi bincike kan kisan yarinya Bafalasɗiniya Hind Rajab

    Rundunar sojin Isra'ila ta fara bincike kan wasu munanan hare-hare biyu da aka kai a Gaza sa'ilin yaƙin da aka tafka - waɗanda suka yi sanadin kashe wata yarinya Bafalasɗiniya ƴar shekara biyar mai suna Hind Rajab da kuma kisan ma'aikatan agaji 15.

    Dukkanin hare-haren biyu sun yi matuƙar jan hankalin duniya.

    Dakarun Isra'ila sun kashe Hind ce bayan ta shafe sa'o'i tana neman agajin masu aikin agaji na Falasɗinawa sa'ilin da take ɓuya a cikin wata mota bayan da aka kashe danginta waɗanda aka yi wa ruwan harsasai.

    Sai dai rundunar sojin ba za ta yi bincike kan kisan da aka yi wa wasu ma'aikatan agaji bakwai masu aiki da ƙungiyar World Central Kitchen a watan Afurilun 2024 ba.

  13. Kotu za ta yanke hukuncin kan yunkurin korar ƴar Najeriya daga Afirka ta Kudu

    Ana sa ran cewa wata kotun yankin Cape Town za ta yanke hukunci a yau game da batun Chidinma Adetshina, ƴar Najeriyar da ta lashe sarauniyar kyau a shekarar 2024, bisa yunkurin hukumomi na mayar da ita Najeriya.

    A watan Yuni ne aka kama Chidinma bayan ta sake shiga Afirka ta Kudu ta kan iyaka da Mozambique.

    Lamarin ya biyo bayan taƙaddama da aka samu game da zaman ta ƴar asalin ƴar Afirka ta Kudu.

    An haifi Chidinma ne a ƙasar ta Afirka ta Kudu, inda mahaifiyarta ƴar ƙasar ce yayin da mahaifinta ɗan Najeriya ne.

    Sai dai taƙaddama ta kaure game da asalinta bayan da ta cancanci zuwa matakin ƙarshe na zaɓen sarauniyar kyau ta Afirka ta Kudu a shekarar 2024.

    Lauyan da ke kare ta na ƙalubalantar tsare ta da aka yi da kuma yunƙurin fitar da ita daga ƙasar yayin da ma'aikatar harkokin cikin gida ta Afirka ta Kudu ta ce ba ta da halastattun takardun ci gaba da zama a ƙasar.

  14. An fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya

    Yau ce ranar farko ta fara yaƙin neman zaɓe a Najeriya gabanin babban zaɓen ƙasar na watan Janairu, yayin da ake nuna damuwa kan matsalar tsaro da ta ƙi ci ta ƙi cinyewa da kuma tsadar rayuwa a ƙasar.

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu na neman wa'adi na biyu sai dai farin jininsa ya yi ƙasa a baya-bayan nan.

    Ɗaya daga cikin manyan ƴan adawa mafi ƙarfi da ke takara da Tinubu shi ne tsohon shugaban ƙasar Atiku Abubakar, sai kuma tsohon gwamna Peter Obi.

    Bankin Duniya ya ce sama da rabin ƴan Najeriya na rayuwa cikin ƙangin talauci.

  15. Iran ta gargaɗi ƙasashen yankin Gulf kan haɗa kai da Amurka

    Rundunar sojin Iran ta gargaɗi ƙasashen yankin Gulf kan haɗa kai da Amurka wajen shirya mata hare-hare.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa X, babban hafsan rundunar sojin ƙasar Iran, Ali Abdollahi ya ce "Ba zai yiwu a jibge ɗimbin jiragen yaƙi, musamman jiragen ɗaukar mai, a yankin ba tare da ƙasashen sun sun sani ba."

    Ya ce Iran za ta ɗauki duk wani "taimako" da aka bai wa sojojin Amurka a matsayin haɗa kai ko bayar da goyon baya ga dakarun Amurka.

    A tsawon lokacin yaƙi tsakanin Iran da Isra'ila tare da Amurka, Iran ta kai hare-hare sau da dama kan sansanonin soji da ke ƙasashen yankin waɗanda ke ƙawance da Amurka.

  16. Laberiya ta amince ta karɓi baƙin da Amurka ta kora

    Laberiya ce ƙasar Afirka ta baya-bayan nan da ta amince ta karɓi baƙin da Amurka ta kora, inda ake sa ran irin waɗannan baƙi guda 20 za su isa ƙasar gobe Alhamis.

    Gwamnatin Laberiya ta ce ta amince ta karɓi baƙin da suka kai 1,200 a ƙarƙashin shirin Amurka na tura baƙin da ta kora zuwa wasu ƙasashe na daban.

    A watan Satumban bara, gwamnatin Laberiya ta amince ta karɓi baƙi waɗanda ƴan asalin ƙasashen Afirka ne da kuma ƴan asalin ƙasashen yankin nahiyar arewaci da kudancin Amurka na shekara ɗaya, bisa dalilai na jin-ƙai.

    Ma'aikatar yada labarai ta ƙasar ta fitar a wata sanarwa cewa ba za a bai wa ƙasar wata lada ba a sanadiyyar hakan sai dai za a taimaka mata wajen tabbatar da samun nasarar shirin da kuma ƙarfafa harkar shige da ficenta.

    Haka nan kuma gwamnatin ƙasar ta Laberiya ta ce za a bai wa baƙin damar neman mafaka a ƙasar idan suna buƙata, kuma za su iya ci gaba da zama a ƙasar idan suna son hakan.

    Aƙalla ƙasashen Afirka 10 ne suka amince su karɓi baƙin da Amurka ta kora a ƙarƙashin shirin gwamnatin Donald Trump na tura baƙi zuwa wasu ƙasashe na daban.

    A mafi yawan lokuta babu cikakken bayani kan irin waɗannan yarjeniyoyi tsakanin Amurka da ƙasashen, sai dai wasunsu sun karɓi ladan kuɗaɗe. Misali, Eswatini ta karɓi kuɗi sama da dala miliyan biyar kan karɓar irin waɗannan baƙin.

  17. Iran ta musanta harba wa Daular Larabawa makamai

    Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin waje ta Iran ya musanta zargin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta yi na cewa Iran ɗin ta harba mata makamai masu linzami.

    Ismael Beqai ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa “zargin na UAE ba shi da tushe balle makama”.

    Mai Magana da yawun na Iran ya ce: “Matakin na Háɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya saɓa da tsarin zama na maƙwaftaka kuma hakan zai iya yin cikas ga yunƙurin da ake yi na yayyafa wutar rikici tsakanin ƙasashen yankin.”

    Sa’o’i bayan Iran ta sanar da cewa ta harba makamai ne ƙasar ta Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta ce ta dakatar da duk wata alaƙa ta kasuwanci ko kuɗi da Iran har sai abin da hali ya yi.

    Tun bayan ɓarkewar yaƙi tsakanin Iran da Amurka, Daular Larabawa ta kasance ƙasar da ta fi shan hare-hare daga Iran a yankin.

  18. Ruftawar mahaƙar ma'adanai ta kashe mutum 107 a Kamaru

    Aƙalla mutum 107 sun mutu sanadiyyar ruftawar ramin haƙar ma'adanai a ƙauyen Zamboi da ke kan iyakar Kamaru da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka, kamar yadda wani jami'i a yankin ya bayyana wa BBC.

    Adamou Abdon, wanda shi ne magajin garin Garoua-Boulai a yankin gabashin Kamaru ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

    "An zaƙulo gawarwaki 107 daga cikin ƙasa," kamar yadda ya shaida wa BBC, inda ya ƙara da cewa lamarin "ya faru ne a wani wurin haƙar ma'adanai da ke bangaren Jamhuriyar Tsakiyar Afirka, kusa da kan iyaka da ƙasar Kamaru."

    Har yanzu babu tabbas kan abin da ya haddasa ruftawar ƙasar. Bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta ya nuna yadda ƙasa ta rufta kan masu haƙar zinare da ke a mahaƙar.

    Ana ƙoƙarin gudanar da aikin ceto a yankin sannan ana fargabar cewa yawan waɗanda suka mutu zai ƙaru.

    Haƙar ma'adanai ɗaya ne daga cikin manyan hanyoyin dogaro na mutanen gabashin Kamaru.

    Sai dai babu yanayi mai kyau a wuraren haƙar ma'adanan, inda a mafi yawan lokuta masu aikin kan fada cikin haɗarin kamuwa da cutuka ko kuma bala'o'i.

    Haka nan kuma ruftawar wuraren haƙar ma'adanai abu ne da ya yawaita a ƙasar.

  19. Tsohon ministan tsaron Ukraine na son a yi sabon zaɓe a ƙasar

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, na fuskantar ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen siyasa ga ikonsa tun bayan fara mamayar da Rasha ta kai wa ƙasar, bayan da tsohon ministan tsaronsa ya yi kira da a gudanar da zaɓe.

    Mykhailo Fedorov, wanda aka kora daga muƙaminsa a watan da ya gabata lamarin da ya haifar da zanga-zanga a sassa daban-daban na ƙasar, ya ce bai kamata dimokuraɗiyya ta zama abin da Rasha za ta iya dakatarwa ba.

    Sai dai dokar ta-ɓaci da ake aiwatarwa a Ukraine tun bayan fara yaƙi har yanzu ta haramta gudanar da zaɓe a lokacin da ake fama da yaƙi.

    Har zuwa yanzu, Shugaba Zelensky bai mayar da martani a hukumance kan kiran da Fedorov ya yi ba. A gefe guda kuma, sojojin Ukraine na ci gaba da kai hare-hare a cikin yankunan Rasha.

    Gwamnan yankin Bashkortostan na Rasha, Radiy Khabirov, ya ce wasu jiragen sama marasa matuƙa na Ukraine sun haddasa gobara a wani wurin masana'antu da ke yankin.

  20. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance da ku daga yanzu zuwa ƙarfe 4 na yamma in sha Allah.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.