Shugaban Kenya ya sake naɗa wasu ministocinsa shida da ya kora a makonnin baya
Shugaban Kenya, William Ruto ya sake naɗa mutum shida daga cikin ministocin da ya kora makonnin da suka gabata.
Mista Ruto ya sanar da sunayen mutum 11 cikin ƙunshin sabbin ministocin nasa, wato kimanin rabin adadin da kundin tsarin mulki ya sahale masa.
Shugaban na Kenya ya ce har yanzu yana ci gaba da tuntuɓa kafa kafa abin da ya kira ''gwamnatin da ta ƙunshi kowa'' a ƙasar.
Daga cikin ministocin da ya sake naɗawa akwai Kithure Kindiki, wanda ya sake komawa kan muƙamin da ya bari a baya na ministan cikin gida.
An yi ta kiraye-kirayen ya sauka daga muƙaminsa sakamakon rawar da ya taka kan yadda 'yansanda suka murƙushe zanga-zangar adawa da ƙarin kuɗin haraji da aka gudanar a makonnin baya-bayan nan, lamarin da ya yi sanadin mutuwar fiye da mutum 40.
An zargi 'yansanda da kamawa tare da muzgunawa masu zanga-zangar.
A farkon wannan wata ne shugaban ya gana da jagoran adawar ƙasar Raila Odinga inda ya bayyana aniyarsa ta kafa kwamiti mai mambobi 150 domin magance matsalolin da ƙasar ke fuskanta.