Houthi ta yi barazanar kai hari kan filayen jiragen sama a Saudiyya
Ƙungiyar Houthi ta Yemen ta yi barazanar kai hare-hare kan filayen jiragen sama da sauran muhimman wurare a Saudiyya idan Riyadh ta ci gaba da abin da ta kira ƙeta sararin samaniyar Yemen.
Kakakin rundunar Houthi, Yahya Saree, ya ce mayaƙansu sun fuskanci jiragen yaƙin Saudiyya da suka yi ƙoƙarin hana wani jirgin saman farar hula na Iran sauka a filin jirgin saman Sanaa.
Ya kuma jaddada cewa zirga-zirgar jirage tsakanin Sanaa da Tehran za ta ci gaba.
Tashar Al-Masirah mai alaƙa da Houthi ta ruwaito cewa wani jirgin Iran ya isa Sanaa a ranar Juma’a ɗauke da wakilan ƙungiyar da suka halarci jana'izar tsohon jagoran Iran, Ali Khamenei, tare da sama da marasa lafiya 200.
A martaninta, ƙawancen sojojin da Saudiyya ke jagoranta ya ce kalaman Houthi wani yunƙuri ne na kau da hankali daga abin da ya kira ayyukan ƙungiyar a Yemen, tare da yin gargaɗin cewa zai mayar da martani mai ƙarfin da ba a taɓa gani ba ga duk wani hari kan Saudiyya.