Wace ce marigayiya Saratu Daso da aka gaza maye gurbinta?, Daso ta cika shekara guda da rasuwa cif-cif
A game da irin giɓin da ta bari a masana'antar Kannywood, fitaccen mai shiryan fina-finai a Kannywood, Alhaji Naziru Auwal, wanda aka fi sani da Ɗan Hajiya ya ce giɓi ne babba wanda da wahala a iya mayewa.
Ya ce, "Hajiya Daso mutum ce wadda take taka rawa ta musamman a fim wanda ba kowa ba ne yake iya takawa. Idan ka duba kusan fim ɗinta na ƙarshe shi ne fim ɗina mai suna Umarni. Mun yi zango na farko da ita ne sai Allah ya yi mata rasuwa."
Ya ce duk da cewa a lokuta da dama idan aka samu irin haka ana musanya jarumi ne, "amma na yi iya dubawar da zan iya, amma har ga Allah ban samu abin da nake so ba, sai dai kawai kwatantawa, haka kawai na haƙura na kashe fitowar. Don haka gaskiya ta bar mana babban giɓi, fatanmu shi ne Allah ya mata rahama," in ji shi.
Dangane da ayyukan jinƙai ma, har yanzu ba a iya maye gurbinta ba.
"A wannan azumin yara suka zo suka sa me ni kan batun kayan Sallah, sai na ce musu ai dama Daso ce ke ba ku yanzu kuma ba ta nan. Ni kuma ba ni da ƙarfin yin abin da take yi." In ji Zinaru Muhammad Giɗaɗo, ƙanwa ga marigayiya Daso.