Gwamnatin jihar Neja ta haramta yawo da gashin dada
Gwamnan jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya, Umar Bago, ya umarci jami'an tsaro da su kama ƴandaba da duk waɗanda ke da hannu wajen tayar da zaune tsaye a Minna, babban birnin jihar.
Bago ya bayar da umarnin ne bayan samun tashe-tashen hankula a birnin na Minna.
Umarnin nasa ya hada da kama mutanen da ke yawo da gashin dada.
Tuni dai gwamnatin jihar ta sanya dokar takaita zirga-zirgar mutane da baburan haya, domin magance rikicin ƴandaba da birnin ke fama da shi.
Lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane goma, kamar yadda rahotanni suka bayyana.