Muna nazarin ci gaba da tattaunawa da Amurka bayan sabbin hare-hare - Iran

Asalin hoton, Tasnim news agency
Iran ta bayyana cewa za ta sake duba yiwuwar ci gaba da tattaunawa tsakanin ta da Amurka bayan sabbin hare-haren da aka ta kai.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana hakan bayan sabuwar musayar wuta tsakanin ƙasashen biyu.
Ya ce, “Harkar diflomasiyya ba ta gudana a cikin yanayi mara tasiri ba, domin ci gaba da kowace tattaunawa, dole ne a samu wani dan sarari da zai ba da damar ci gaba da aiwatar da ita.”
Baghaei ya zargi Amurka da “lalata tsarin tattaunawar ta hanyar aika sakonni masu karo da juna da sauya matsaya akai-akai, da kuma karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau da dama.”
A safiyar ranar Laraba ne Amurka ta kai hare-haren sama a wasu wurare a kudancin Iran, a matsayin martani ga harbo jirgin yaƙinta da Iran ta yi a tekun Oman.
A gefe guda kuma, sansanin Khatam al-Anbiya ya sanar da cewa sojojin juyin juya halin Iran sun kai hari a kan sansanonin Amurka da ke kasashen Bahrain, Kuwait da Jordan.















