Isra'ila da Hamas sun amince da sharuɗan Trump na tsagaita wuta a Gaza
Hamas ta ce ta samu wasu dabaru daga wajen Amurka ta hanyar masu shiga tsakani a kan yadda za a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.
Hamas ta fitar da wata sanarwa bayan shugaba Donald Trump ya gabatar da abin da ya kira gargadi na karshe ga Hamas din akan ta amince da cimma yarjejeniya ta saki Isra'ilawan da take tsare da su.
Wakiliyar BBC ta ce tun da farko shugaban Amurkan ya wallafa a shafinsa na sada zumunta cewa Isra'ila ta amince da sharudansa, yanzu ya ragewa Hamas ita ma ta amince da sharudan.
A cewar kafar yada labaran Isra'ila, abin da kunshin yarjejeniyar baya-bayan nan ya kunsa shi ne Hamas za ta saki dukkan mutanen da take tsare da su su 48 wanda yawancinsu an kashe su a ranar farko da yarjejeniyar za ta fara aiki, inda kuma za a sako dubban Falasdinawa fursunoni a matsayin musaya.
Akwai kuma tattaunawar da za a yi akan kawo karshen yakin da ake yi gaba daya.