Iran ta ce ta kai hari tare da lalata sansanin sojin Amurka da ke Kuwait

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar Juyin Juya halin Iran (IRGC) ta sanar da sake kai hari kan sansanin sojin Amurka na Al-Adiri da ke Kuwait, inda ta ce ta banka wa rumbunan adana makamai da kayan aiki guda uku wuta.
A cikin sanarwar IRGC ya bayyana cewa ta kai hari kan hasumiyar sa ido ta rundunar ruwa ta biyar ta Amurka da ke Bahrain, tare da lalata ta.
Har zuwa yanzu, babu wani martani daga Amurka kan wannan rahoto.
A cikin makonni biyu da suka gabata, an kai hare-hare sau da dama a wasu wurare a Bahrain da Kuwait da ake dangantawa da Iran.
Iran ta ce sansanoni da kadarorin Amurka da ke yankin suna cikin halastattun wuraren da za ta iya kai wa hari.






















