Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 03/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Najeriya ta kwashe ƙarin mutanenta 266 daga Afirka ta Kudu

    Ƴan Najeriya sama da 260 sun isa birnin Legas a safiyar Juma'a yayin da gwamnatin ƙasar ke ci gaba da kwashe mutanenta da ke zaune a Afirka ta Kudu sanadiyyar zanga-zangar ƙyamar baƙi da ta ɓarke a baya-bayan nan.

    Yanzu yawan ƴan Najeriya da gwamnatin ƙasar ta kwashe daga ƙasar ta Afirka ta Kudu ya kai 700.

    Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin waje ta Najeriya Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya shaida wa BBC cewa mutane 266 ɗin da suka isa Najeriya a yau sun sauka birnin Legas ne da ƙarfe 10:40 na safe.

    Najeriya ta fara kwashe mutanenta daga Afirka ta Kudu ne bayan jerin zanga-zangar da wasu ƙungiyoyi suka riƙa yi, inda suke far wa baƙi, lamarin da ya sa ƴan Najeriya mazauna Afirka ta Kudu suka riƙa kira ga gwamnatinsu da ta kwashe su zuwa gida.

    Wannan ne jirgi na huɗu na ƴan Najeriya da ya isa gida a ƙarƙashin shirin.

    Hukumomin Najeriya sun kuma ce akwai wasu jiragen ɗauke da ƴan Najeriya da ake sa ran za su sauka a ƙasar a ranakun 6 da kuma 9 ga watan Yuli.

    Haka nan gwamnatin Najeriyar ta shawarci ƴan ƙasar nata da ake mayarwa gida su tantance dukiyoyinsu da suka bari a baya, inda hukumomin ke sa ran neman gwamnatin Afirka ta Kudu ta biya diyya.

  2. Wakilan ƙasashen duniya sun halarci taron jana'izar Ayatollah Ali Khamenei

    An fara gudanar da tarurrukan jana'izar shugaban Iran a birnin Tehran, tare da halartar baƙi da manyan jami'ai daga ƙasashen waje.

    Tun da farko an wallafa hotunan He Wei, mataimakin shugaban babban majalisar Jama'ar China wanda ya isa Tehran domin halartar taron da za a gudanar a yau.

    A farkon ziyararsa, ya kuma gana da Mohammad Bagher Qalibaf, kakakin majalisar dokokin Iran.

    Ya zuwa yanzu, shugaban ƙasar Turkmenistan da kakakin majalisar dokokin Iraƙi, da shugaban kasar Iraƙi, da shugaban yankin Kurdistan na Iraki, da firaministan Armenia na daga cikin waɗanda za su halarci taron jana'zar.

    Za a ci gaba da gudanar da tarurrukan jana'izar, wanda ƴan ƙasa da masu jimami za su halarta, a ranar Litinin a Tehran, da ranar Talata a Qom da ranar Laraba a Iraƙi, da kuma ranar Alhamis a Mashhad.

    Shugaban ƙasar Tajikistan, Emomali Rahmon, ya isa birnin Tehran da safiyar ranar Juma'a domin halartar jana'izar Ali Khamenei.

  3. Hukumomin Najeriya sun tabbatar da janyewar sojojin Amurka daga ƙasar

    Najeriya ta tabbatar da janyewar akasarin sojojin Amurka da aka tura ƙasar a farkon wannan shekarar don taimakawa wajen yaƙi da ƙaruwar ayyukan ta'addanci daga ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

    Kakakin rundunar sojin Najeriya, Michael Onoja, ya shaida wa BBC ranar Juma'a cewa "ba zai shafi yadda muke tafiyar da harkokinmu ba ." Ya kuma ce "Za mu ci gaba da musayar bayanan sirri", yana mai maimaita kalaman da kwamandan rundunar sojin sama ta Amurka a Afirka, Janar Dagvin Anderson, wanda ya yi a lokacin wani taron manema labarai a ranar Alhamis.

    Najeriya na fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, ciki har da ƙungiyoyi masu dauke da makamai masu iƙirarin jihadi da ƴan fashin daji da kuma tashe-tashen hankulan da suka bazu daga arewa zuwa sassan tsakiya da kudancin Najeriya.

    Haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Amurka ya ƙaru bayan da Washington ta zargi hukumomin Najeriya da rashin yin abin da ya dace don kare ƙungiyoyi masu rauni, kuma ta yi zargin cewa ana yi wa "kiristoci kisan ƙare dangi" a ƙasar - ikirarin da Najeriya ta miusanta, tana mai cewa tashin hankalin yana da sarkakiya kuma yana shafar mutane a dukkan al'ummomi.

    Tun daga watan Disamba na shekarar da ta gabata, ƙasashen biyu sun ce dakarunsu sun gudanar da ayyukan haɗin gwiwa don kai hari kan maɓoyar ƴan bindiga a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa tsaro a Najeriya.

  4. An ceto mutumin da ya tsira daga girgizar ƙasa a Venezuela bayan kwana takwas

    An ceto wani mutum da ransa bayan ya maƙale na tsawon kwanaki takwas a ƙarƙashin ɓaraguzan ginin da ya ruguje bayan girgizar ƙasa ta biyu da aka yi a ƙasar Venezuela.

    Ma'aikatan aikin gaggawa sun sami nasarar zaƙulo Hernán Gil sama da sa'o'i 100 bayan da suka gano shi a ƙarƙashin tan 140 na tarkace.

    Shugabar riƙo ta ƙasar Venezuela Delcy Rodríguez ta ziyarci Gil a asibiti a ranar Alhamis.

    Ya zuwa yammacin Alhamis, an tabbatar da mutuwar mutum 2,595 a girgizar ƙasar da ta afku a Venezuela a ranar 24 ga Yuni, kuma har yanzu akwai dubban mutane da ba a gano inda su ke ba.

    Da ta ke magana a wani taron manema labarai a ranar Alhamis, Rodríguez ta bayyana girgizar ƙasar a matsayin "wani bala'i mai munin da bamu taba tsammani ba".

    Ta yi watsi da sukar da da ake yi cewa gwamnatinta ba ta gaggauta ɗaukar matakai bayan girgizar ƙasar ba, tana mai cewa an tura dubban jami'ai bayan aukuwar bala'in.

  5. Adadin waɗanda suka mutu a harin da Rasha ta kai kan Ukraine ya kai 30

    Sojojin Rasha sun kai wani mummunan harin makami mai linzami kan Kyiv cikin daren Alhamis, inda suka kashe aƙalla mutum 30, abin da magajin garin ya bayyana a matsayin "hari mafi muni" da aka kai babban birnin Ukraine.

    Mutum 91 sun ji rauni, in ji shugaban gwamnatin sojin Kyiv, Timur Tkachenko.

    Magajin gari Vitaly Klitschko ya ce wata tashar motocin asibiti na daga cikin wuraren da abin ya shafa.

    Duk da cewa hare-haren da aka kai a baya sun yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, wannan harin shi ne wanda ke da mafi yawan bama-bamai da aka zazzaga a babban birnin ƙasar.

    An kwashe mutane daga unguwanni da dama yayin da aka kai hare-hare a birnin sa'o'i bayan shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya gargaɗin cewa Rasha na shirin kai hari.

    Moscow ta ce dakarunta sun kai hari kan abin da ta kira masana'antar soji a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren da ake kai wa farar hula a Rasha.

    Kakakin Kremlin Dmitry Peskov ya shaidawa manema labarai jiya Alhamis cewa, Rasha za ta ci gaba da ƙara matsawa gwamnatin Kyiv lamba har sai ta cimma muradunta.

  6. Iran ta fara makokin Ayatollah yayin da ake shirye-shryen jana'izarsa

    Iran ta fara gudanar da zaman makoki na gama-gari yayin da ake shirin fara jana'izar tsohon Jagoran addinin kasar, Ayatollah Ali Khamenei, bayan fiye da watanni huɗu da aka kashe shi a hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai.

    Za a ajiye gawar tsohon Ayatollah din a babban ɗakin taro na 'Grand Mosalla' da ke birnin Tehran tun daga ranar Juma'a, kafin a kai shi garinsu na Mashhad domin binne shi a ranar Alhamis mai zuwa.

    Jami'ai sun ce jana'izar na iya samun halarcin masu makoki miliyan 20 daga sassan Iran, a cewar AFP.

    Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen Iran da Amurka ke tsagaita wuta a tsakaninsu bayan sanya hannu kan yarjejeniyar farko ta dakatar da faɗan da suke yi a watan Yuni.

    Za a ajiye gawar Khamenei a Grand Mosalla na tsawon kwanaki uku, tare da gawarwakin sauran yan daginsa da aka kashe a harin da Amurka da Isra'ila suka kai a watan Fabrairu.

    Za a yi wani taron jana'iza a hukumance a birnin Tehran ranar Asabar.

    Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewa hukumomi sun umarci ofisoshin gwamnati da na masu zaman kansu da ke Tehran da su rufe daga Asabar zuwa Litinin, yayin da aka kafa dokar takaita zirga-zirga a sassan tsakiyar birnin.

  7. Harin bam ya kashe mutum shida a Syria

    Kafafen yaɗa labaran gwamnatin Syria sun ce wani bam ya tashi a wani gidan shan shayi mai cike da jama'a a tsakiyar birnin Damascus, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum shida tare da jikkata wasu 22.

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta ce an dasa wani abu mai fashewa a cikin gidan shayin, wanda ke da nisan mita 100 kacal (ƙafa 330) daga ginin ma'aikatar Shari'a, wani babban ginin gwamnati a gundumar Hejaz da ke babban birnin ƙasar.

    Babu wata ƙungiya da ta yi ɗauki alhakin kai harin nan take. Wannan shi ne harin bam mafi muni da aka kai a birnin Damascus tun bayan harin ƙunar baƙin wake da aka kai a wani coci a watan Yunin 2025 wanda ya kashe mutane 25.

    Wata kungiyar masu iƙirarin jihadi mai suna Saraya Ansar al-Sunnah, ta ce ita ce ta kai harin, amma hukumomi sun dora alhakin harin kan ƙungiyar IS.

    Mohammed al-Dahabi, mamallakin wani shagon sayar da gilashi da ke kusa da gidan shayin, ya ce harin bam ɗin na ranar Alhamis ya yi kama da wanɗnada aka riƙa gani a Damascus a lokacin yaƙin basasar Syria.

    A yayin ziyarar da ya kai wurin da lamarin ya faru, Gwamnan Damascus, Maher Marwan Idlibi, ya ce za a hukunta waɗanda ke da hannu a kitsa harin.

  8. Assalamu Alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.