Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 30 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Rukuni na uku na ƴan Najeriya da aka kwashe daga Afrika ta Kudu ya isa Lagos

    Rukuni na uku na ‘yan Najeriya da aka kwashe daga kasar Afirka ta Kudu sun isa birnin Lagos, yayin da gwamnati ke ci gaba da kokarin dawo da ‘yan kasar cikin aminci.

    Jirgin da ya kawo su ya sauka ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammed, inda jami’an gwamnati da na kula da ‘yan gudun hijira suka tarbe su.

    Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce waɗanda aka dawo da su sun kai 264 wanda ya haɗa da maza, mata da yara,

    Wasu daga cikin wadanda suka iso sun ce sun sha wahala sakamakon rashin tsaro, da kuma takurawa rayuwa a wasu yankunan kasar ta Afirka ta Kudu.

    An fara kwaso mutanen ne bayan shafe makonni ana zanga-zangar ƙyamar baƙi a wasu sassan Afirka ta Kudu, da kuma cikar wa’adin ranar 30 ga Yuni da masu zanga-zangar suka bai wa baƙin da ba a wa rijistar zama a ƙasar ba su bar ƙasar. Lamarin ya janyo wasu ‘yan Afirka neman taimakon komawa ƙasashensu.

    A baya, kusan mutum 270 aka dawo da su a jirgin farko, yayin da kusan 66 suka biyo baya a rukuni na biyu. Wasu ‘yan Najeriya na cewa zanga-zangar ta bar su cikin damuwa da rashin tabbas kan makomarsu.

    Kakakin ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa, ya ce gwamnati ta shirya kwaso mutanen ne saboda kare lafiyarsu, yana mai cewa duk wanda ya yi rajista don dawowa shi dole ne a taimaka masa.

    Ya kuma bayyana cewa an shirya karin jirage uku a ranakun 3, 6 da 9 ga Yuli ga waɗanda suka yi rajista suna son a dawo da su.

    Gwamnati ta shawarci ‘yan Najeriya da ke can da su bi dokokin ƙasar kuma su guji rikici, tana mai lura da yadda lamura ke tafiya.

  2. Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 13 a Ghana

    Aƙalla mutum 13 ne suka mutusakamakon ambaliyar ruwa da ta afku a babban birnin Ghana, Accra, bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka yi a ranar Litinin.

    Ambaliyar ta kuma lalata gidaje da kadarori da dama.

    Hukumar kashe gobara ta ƙasar ta ce ana fargabar yawan mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa yayin da ake ci gaba da aikin ceto.

    Bidiyoyi da ke yawo a kafafen sada zumunta sun nuna gidaje da motoci sun nutse a cikin ruwa, musamman a ƙananan yankuna da suka fi fama da ambaliyar, lamarin da ya haddasa tsaikon zirga-zirga.

    Duk da cewa yawancin ruwan ya ragu, mutanen da abin ya shafa na ci gaba da ƙididdige asarar da suka yi.

    Shugaban ƙasar, John Mahama, ya bayar da umarnin rusa dukkan gine-ginen da aka yi a hanyoyin ruwa, yana mai cewa irin waɗannan ayyuka na jefa al’umma cikin haɗari.

    Haka kuma ya bayyana cewa ana samun ƙaruwa a yawan ruwan sama sakamakon sauyin yanayi, inda aka samu milimita 140 na ruwan sama a rana guda, fiye da adadin da aka samu a bara.

    Gwamnatin ƙasar ta shawarci mazauna yankunan da abin ya shafa su koma wurare mafi tsaro, tare da gargadin direbobi da su guji hanyoyin da ruwa ya mamaye.

    Ambaliyar ta kuma katse wutar lantarki a wasu sassan birnin, yayin da aka tura jami’an tsaro da na agaji domin taimakawa waɗanda iftila'in ya shafa.

  3. Za a yi sauye-sauye a tsarin shirin NYSC

    Majalisar zartarwa ta Najeriya (FEC) ta amince da yin manyan sauye-sauye a tsarin shirin bautar ƙasa na NYSC, ciki har da mayar da shugabancinsa hannun farar hula maimakon sojoji, da kuma tsawaita lokacin atisaye a sansani daga makonni uku zuwa shida.

    An cimma wannan matsaya ne a taron FEC na ranar Litinin a Abuja, wanda shi ne karo na farko da aka yi cikakken bita ga shirin tun bayan kafa shi a shekarar 1973.

    A ƙarƙashin sabon tsarin, farar hula za su jagoranci harkokin NYSC, yayin da sojoji za su ci gaba da bayar da tsaro ga masu yi wa ƙasa hidima.

    Gwamnatin tarayya ta kuma umarci Babban Lauyan Ƙasa da Ma’aikatar kula da ci gaban matasa su gyara dokar NYSC da sauran ƙa’idoji domin bai wa sauye-sauyen cikakken tushe na doka.

    Ministan kula da matasa, Ayodele Olawande, ya ce an aiwatar da wannan matakin ne domin inganta NYSC ya koma shiri da ke haɓaka ƙwarewa da samar da damar aikin yi.

    Ya ƙara da cewa za a ɓullo da tsarin kiran masu yi wa ƙasa hidima da tura su bisa la’akari da tsaro, tare da mai da hankali kan koyar da shugabanci da kasuwanci da ƙwarewar zamani.

  4. Ba mu yarda da maƙiyanmu ba, zaune muke a shirye - Iran

    Ministan tsaron Iran na riƙo ya ce ƙasar ba ta yarda da maƙiyanta ba, kuma zaune ƙsar take a shirye wajen fuskantar duk wani hari, yana gargadin cewa idan aka karya yarjejeniyar tsagaita wuta za su mayar da martani cikin gaggawa da ƙarfi.

    A cewarsa, Iran a shirye take ta kare kanta a kowane lokaci, inda ya jaddada cewa rundunar ƙasar na cikin cikakken shirin tunkarar duk wani hari daga waje.

    Wannan jawabi ya zo ne yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan Qatar kuma ministan tsaro, inda ɓangarorin biyu suka tattauna batutuwan tsaro da kuma yiwuwar ƙara haɗin gwiwar tsaro tsakaninsu.

    Ministan ya kuma nuna damuwa kan yadda wasu ƙasashen waje ke shiga harkokin yankin, yana mai cewa hakan ba ya samar da tsaro sai dai yana ƙara rikici da rashin amincewa tsakanin ƙasashe, yana mai kira da a bar ƙasashen yankin su kula da tsaronsu da kansu.

    Wannan dai na zuwa ne yayin da rikici ya ƙaru tun bayan hare‑haren Amurka da Isra’ila a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya sa Iran ta mayar da martani har da kai farmaki kan wasu wurare a Qatar.

    A yanzu haka, Qatar tare da Pakistan na ƙoƙarin shiga tsakani domin samar da yarjejeniyar zaman lafiya ta dindindin tsakanin Iran da Amurka.

  5. Ba mu tsara wata tattaunawa da Amurka ba a Doha - Iran

    Iran ta musanta iƙirarin Trump cewa za a fara sabbin tattaunawa da Amurka a Doha, tana mai cewa ba ta tsara wata ganawa ko tattaunawa da Amurka ba a wannan lokaci ba.

    Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce wakilan ƙasar da ke tafiya Doha ba don tattaunawa ba ne, sai dai domin bibiyar batun kuɗaɗen ƙasar da aka ƙwace a ƙasashen waje.

    Wannan matsaya na Tehran ya zo ne duk da cewa Trump ya bayyana cewa za a gudanar da ganawa tsakanin wakilan ƙasashen biyu a babban birnin Qatar.

    Sai dai jami’an Iran sun musanta wannan batu, suna jaddada cewa babu wani shiri na ganawa ko tattaunawa da suka shirya yi da Amurka a kwanaki masu zuwa.

    A wani ɓangare, Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kimanin dala biliyan 6 daga cikin biliyan 12 na kuɗaɗen Iran da aka ƙwace za su sake dawowa da su hannun gwamnati nan ba da jimawa ba.

    Ya ce ana ci gaba da bin matakan da suka dace domin ganin an saki kuɗaɗen, wanda ake ganin zai taimaka wajen karfafa tattalin arzikin ƙasar.

    Haka kuma, Iran ta yi martani ga bayanan da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi, inda ta jaddada cewa ita kaɗai ce ke da ikon gudanar harkokin mashigin Hormuz.

  6. An fara zanga-zangar ƙyamar baƙi a Afrika ta Kudu bayan cikar wa'adi

    An fara zanga‑zangar ƙyamar baƙi a sassa daban‑daban na Afirka ta Kudu, lamarin da ya sa aka jibge jami’an tsaro saboda fargabar rikice‑rikice.

    Shugaba Cyril Ramaphosa ya buƙaci masu zanga‑zangar su guji tashin hankali, yana mai jaddada cewa dole ne a gudanar da zanga‑zanga cikin lumana ba tare da tsoratarwa ba.

    Zanga‑zangar na da alaƙa da wa’adin da wasu ƙungiyoyi suka bai wa baƙin da ba su da rijistar zama cikin ƙasar da su fice.

    Hakan ya sa mutane da dama suka fara tserewa saboda tsoron hare‑hare, yayin da hukumomi suka ce an riga an mayar da sama da mutum 25,000 kasashensu, yawancinsu daga wasu ƙasashen Afirka.

    A birnin Johannesburg, inda ake gudanar da wasu daga cikin zanga‑zangar, an samu tsaiko a harkokin yau da kullum, inda shaguna da dama suka rufe, kuma aka samu yanayi na tsoro da shiru.

    Dubban baƙi kuma na cigaba da jiran a kwashe su a sansanonin wucin gadi domin tsira da lafiyarsu.

    A gefe guda, Shugaba Ramaphosa ya tunasar da jama’a cewa baƙin da ke zaune bisa doka na da haƙƙi kamar kowa, yana mai cewa suna taka muhimmiyar rawa wajen gina tattalin arziƙin ƙasar.

    A Durban kuwa, ana rushe sansanonin da ke ɗauke da ‘yan Malawi, yayin da wasu ke bayyana takaicinsu na barin iyalansu da rayuwar da suka fara ginawa sakamakon matsin lamba da matsalar tsaro.