Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Talata 12/05/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. A binciki "asarar rayuka fiye da 100" sanadin harin soji a Zamfara - Amnesty

    Kungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International ta buƙaci hukumomin Najeriya su gudanar da bincike kan harin da sojoji suka kai ta sama wanda rahotanni suka ce ya kashe aƙalla farar hula 100 a kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara.

    A cewar ƙungiyar, tun da ƙarfe 12 na ranar Lahadin da ta gabata ne aka ga jiragen yaƙin soji suna shawagi a saman kasuwar da ke ci mako-mako, kafin su sake dawowa su fara ruwan bama-bamai da misalin ƙarfe 2 na rana.

    Daraktan ƙungiyar Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sanusi, ya ce bisa bayanan da suka tattara, kusan duka waɗanda abin ya shafa farar hula ne.

    "Iran wannan ce ta faru a watan da ya gabata a wani gari tsakanin Borno da Yobe inda aka ka hari a kasuwa aka kashe mutum 10 a harin, cikin waɗanda aka kashe har yanzu ba a samu sheda cewa akwai waɗanda ake zargi mayaƙa ba ne." in ji Isa Sanusi.

    Ya ƙara da cewa a makon da ya gabata ma an samu irin wannan lamari a jihar Neja, inda mutane aƙalla 12 suka rasa ransu - yawancinsu ƙananan yara.

    A cewarsa, tun daga shekarar 2017 ake samun irin wannan lamari a arewa maso gabashin Najeriya musamman a jihar Borno inda a cewarsa,ana kai hare-hare da sunan yaƙi da Boko Haram.

    "Ya kamata gwamnati ta tsaya a yi magana da sojoji, kada aikinsu ya zama sanadin asarar rayukan farar hula da mutanen da ba su ji ba su gani ba." in ji shi.

    A cewarsa, a tsarin doka ta ƙasa ta ƙasa ta ƴancin ɗan'adam, bai kamata a cutar da farar hula ba a duk wani aikin samar da tsaro.

  2. Za mu mayar da martani idan aka kai mana hari - Iran

    Iran ta ce dakarunta a shirye suke su mayar da martani kan duk sabbin hare-hare da za a kai mata, bayan da Shugaba Donald Trump ya ce a halin yanzu yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ƙasashen tana tangal-tangal.

    Kakakin majalisar ƙasar Mohammad Ghalibaf ya ce Iran a shirye take ta fuskanci duk wani abin da ka iya faruwa.

    Wakilin BBC ya ce babbar tambaya a nan ita ce yanzu za a ci gaba da tattaunawa ne ko kuma za a koma a ci gaba da artabu.

    Tun da farko Mista Trump ya yi watsi da daftarin zaman lafiya na baya-bayan nan da Tehran ta gabatar kuma ya ce har yanzu yana fatan samun cikakkiyar nasara.

    Farashin ɗanyen mai dai ya tashi a kasuwar duniya ne bisa fargabar za a ci gaba da gwabza faɗa a yankin na gabas ta tsakiya.

  3. Salam Alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa na Kai Tsaye, barka da safiyar wannan rana ta Talata.

    Kamar kodayaushe, shafin zai kawo muku labaran da suka shafi yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi kan Iran da abubuwan da suka shafi Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

    Kuna iya zuwa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu rahotannin da ma kallon bidiyo.