A binciki "asarar rayuka fiye da 100" sanadin harin soji a Zamfara - Amnesty
Kungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International ta buƙaci hukumomin Najeriya su gudanar da bincike kan harin da sojoji suka kai ta sama wanda rahotanni suka ce ya kashe aƙalla farar hula 100 a kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara.
A cewar ƙungiyar, tun da ƙarfe 12 na ranar Lahadin da ta gabata ne aka ga jiragen yaƙin soji suna shawagi a saman kasuwar da ke ci mako-mako, kafin su sake dawowa su fara ruwan bama-bamai da misalin ƙarfe 2 na rana.
Daraktan ƙungiyar Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sanusi, ya ce bisa bayanan da suka tattara, kusan duka waɗanda abin ya shafa farar hula ne.
"Iran wannan ce ta faru a watan da ya gabata a wani gari tsakanin Borno da Yobe inda aka ka hari a kasuwa aka kashe mutum 10 a harin, cikin waɗanda aka kashe har yanzu ba a samu sheda cewa akwai waɗanda ake zargi mayaƙa ba ne." in ji Isa Sanusi.
Ya ƙara da cewa a makon da ya gabata ma an samu irin wannan lamari a jihar Neja, inda mutane aƙalla 12 suka rasa ransu - yawancinsu ƙananan yara.
A cewarsa, tun daga shekarar 2017 ake samun irin wannan lamari a arewa maso gabashin Najeriya musamman a jihar Borno inda a cewarsa,ana kai hare-hare da sunan yaƙi da Boko Haram.
"Ya kamata gwamnati ta tsaya a yi magana da sojoji, kada aikinsu ya zama sanadin asarar rayukan farar hula da mutanen da ba su ji ba su gani ba." in ji shi.
A cewarsa, a tsarin doka ta ƙasa ta ƙasa ta ƴancin ɗan'adam, bai kamata a cutar da farar hula ba a duk wani aikin samar da tsaro.