Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 20 ga watan Yuni, 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. 'Ƴan jarida za su fara yi wa sojoji rakiya wajen ayyukan tsaro'

    Gwamnatin Najeriya na nazarin wani sabon tsari da zai saka 'yan jarida yi wa sojoji rakiya yayin wasu zaɓaɓɓun ayyukan tsaro kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

    An ce wannan mataki na da nufin inganta yadda ake ruwaito harkokin tsaro tare da bai wa jama’a damar fahimtar ainihin abin da ke faruwa a fagen yaki da ta’addanci da sauran barazanar cikin gida.

    Ministan tsaro, Janar Christopher Musa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a wani taron tsaro na kasa da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) ta shirya a Abuja.

    Ya ce wannan tsari zai kara dankon zumunci tsakanin kafafen yada labarai da hukumomin tsaro tare da karfafa gaskiya da fahimta a ayyukan soji.

    Ya kara da cewa rawar da kafafen yada labarai ke takawa ba karama ba ce wajen gina fahimtar jama’a game da harkokin tsaro da tabbatar da zaman lafiya a kasa.

    A cewarsa, a wannan zamani, yaki ba wai kawai a filin daga ake gwabzawa ba, har ma yana da nasaba da bayanai da labaran da ake yadawa, wanda ke sanya ‘yan jarida zama muhimman abokan hulda a tsarin tsaron kasa.

    Ministan ya jaddada cewa nasarar ayyukan tsaro ba wai kawai auna ta ne da nasarorin soji ba, har ma da yadda jama’a ke da yarda da hukumomin tsaro.

    Ya kara da cewa ingantacciyar hadin gwiwa tsakanin ‘yan jarida da jami’an tsaro za ta taimaka wajen kawar da yada jita-jita, sabani a rahotanni, da kuma kara amincewar jama’a yayin da Najeriya ke fuskantar kalubalen tsaro daban-daban.

  2. Cimma yarjejeniya da Iran ta ceci tattalin arziƙin duniya – Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya kare sabon yarjejeniyar da aka cimma da Iran, yana mai cewa ta ceci duniya daga fadawa cikin matsananciyar koma bayan tattalin arziki.

    A wata hira da shafin labarai na Axios, Trump ya bayyana cewa rikicin da ke tsakanin bangarorin ka iya haddasa “durkushewar tattalin arziki ta duniya,” amma yarjejeniyar da suka kulla ta dakatar da hakan.

    Trump ya ce yarjejeniyar da aka cimma na daga cikin abubuwan da za su iya jefa tattalin arzikin duniya cikin hadari idan ba a shawo kansu ba.

    A cewarsa, matakin da ya dauka ya taimaka matuka wajen kauce wa irin wannan matsala, yana mai jaddada muhimmancin yarjejeniyar wajen samar da kwanciyar hankali a tattalin arziki.

    A wata fuska ta daban, Trump bai kawar da yiwuwar daukar irin wannan mataki kan kasar Cuba ba, yana mai cewa hakan “na iya yiwuwa.” Ya kuma sake kare matakinsa na janyewa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015, yana mai cewa da ba a soke yarjejeniyar ba, da Isra’ila ba za ta wanzu ba a yau..

  3. Ministan harkokin wajen Iran zai tafi Switzerland domin shiga tattaunawar zaman lafiya da Amurka

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, na shirin tafiya zuwa ƙasar Switzerland a ranar Asabar domin shiga tattaunawar zaman lafiya da Amurka, kodayake har yanzu ba a tabbatar da jadawalin tafiyar ba kuma ana iya samun sauyi.

    Rahoton Axios ya nuna cewa Araqchi ya bayyana wa wasu jakadun ƙasashe masu shiga tsakani cewa tsagaita wuta a Lebanon shi ne muhimmin abin da zai ƙayyade ko tattaunawar Iran da Amurka za ta ci gaba ko a’a.

    A lokaci guda, wakilin Fadar White House Steve Witkoff na kan hanyarsa ta zuwa Switzerland, yayin da Jared Kushner, wani babban jami’in gwamnatin Amurka, ya riga ya isa ƙasar.

    Ana sa ran fara zagaye na farko na tattaunawar a yankin Bürgenstock, duk da cewa ba a bayyana takamaiman ranar farawa ba.

    Rahotanni sun kuma nuna cewa sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, zai ziyarci Gabas ta Tsakiya nan gaba kadan domin ƙara ƙoƙarin diflomasiyya.

    Iran ta jaddada cewa dole ne a tabbatar da tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hezbollah na Lebanon kafin ta shiga tattaunawar, inda majiyoyi suka ce hakan shi ne sharadin ci gaba da shirin zaman lafiya.

  4. Isra’ila ta kashe mutum biyar a hare-hare a Lebanon duk da amincewa da tsagaita wuta

    Akalla mutum biyar sun mutu a sabbin hare-haren sama da Isra’ila ta kai a kudancin Lebanon, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka sanar da ita tsakanin Isra’ila da kungiyar Hezbollah.

    Hare-haren sun faru ne a yankin Nabatiyeh, inda jiragen yaki da makamai masu linzami suka lalata gidajen fararen hula.

    Rahotanni sun ce an ci gaba da harba bindigogi da manyan makamai a yankin, abin da ke kara nuna irin raunin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma bayan takun-saka mai tsanani.

    Lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da ake kokarin ci gaba da tattaunawar zaman lafiya tsakanin Amurka da Iran a kasar Switzerland, wadda sabbin rigingimun Lebanon ke barazana ga nasararta.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa barkanmu da ganin safiyar yau Asabar.

    Kamar kullum, a yau ma za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya a wannan shafin namu na BBC Hausa kai tsaye.

    Aisha Bbabangida ke fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na Facebook da X da kuma Whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.