An miƙa wa Amurka daftarin sasanta DR Congo da Rwanda
Mai bai wa shugaban Amurka, Donald Trump shawara na musamman kan harkokin Afrika, Massad Boulos, ya tabbatar da karɓar daftarin sasanta ƙasashen DR Congo da Rwanda bayan rsaka hannu kan sharuɗa a tsakaninsu a birnin Washington ranar 25 ga Afrilu.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a jiya, Boulos ya ce: “Na karɓi daftarin sasantawa ɗauke da shawarwarin zaman lafiya daga DRC da Rwanda. Wannan muhimmin mataki ne wajen cika alƙawuran da aka ɗauka a Sanarwar Ka’idoji, kuma ina sa ran ƙasashen biyu za su ci gaba da jajircewa don ganin an samu zaman lafiya.”
Ministan harkokin wajen Rwanda, Olivier Nduhungirehe, ya bayyana cewa har yanzu ba a haɗa ra’ayoyin ƙasashen biyu gaba ɗaya ba, amma ya nuna fatan cewa yarjejeniyar ƙarshe za a iya sanya hannu akanta a fadar White House nan da watan Yuni.
Hukumomin DR Congo ba su fitar da wata sanarwa ba kan takardun, sai dai Shugaba Félix Tshisekedi ya musanta zargin cewa ya sayar da dukiyar ma’adinan ƙasar don samun goyon bayan Amurka a yaƙi da mayaƙan M23 da ake zargin Rwanda na goyon baya gare su.