Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/06/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Rufewa

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin na BBC Hausa, da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, a nan za mu rufe shafin na yau Litinin- 23 ga watan Yuni, 2025.

    Da fatan za ku kasance da mu gobe Talata idan Allah ya kai mu lafiya.

    Amma za ku iya ziyartar shafinmu na bbchausa.com domin ci gaba da karanta labarai da kuma kallon bidiyo da sauransu.

    Mu rufe da wannan karin maganan - A juri ɓara ...

  2. Iran ta ce mutane aƙalla 500 hare-haren Isra'ila suka kashe a ƙasar

    Hukumomi a Iran sun ce mutane aƙalla 500 aka kashe tun bayan da Isra'ila ta fara yi mata luguden wuta, kwanaki goma da suka wuce.

    Haren-haren Isra'ila na baya-bayan nan a birnin Tehran sun faɗa ne a kan gine-ginen gwamnati, ciki har da gidan yarin Evin.

    Isra'ila ta kuma kai hari a kan hanyar shiga babbar cibiyar nukiliya ta Iran, wajen da Amurka ta kai hari a jiya Lahadi.

    Hukumar kula da nukiliya ta duniya (IAEA) ta ce dole ne a ba ta damar shiga cibiyar domin tantance ɓarnar da aka yi.

  3. Shugaban Syria ya sha alwashin hukunta waɗanda suka kai hari coci

    Shugaban riƙon-ƙwarya na Syria, Ahmed Al-Sharaa ya yi alƙawarin hukunta duk masu hannu a harin da aka kai wa wani coci, jiya Lahadi a babban birnin ƙasar, Damascus.

    Mutane aƙalla 25 aka kashe a harin, wanda aka alaƙanta da ƙungiyar IS.

    Wannan ne hari na farko irinsa, da aka kai Syria tun bayan hamɓarar da gwamnatin Shugaba Bashar al Assad.

    Al-Sharaa, wanda tsohon kwamandan masu iƙirarin jihadi ne, ya sha alwashin samar da kariya ga mabiya addinai marassa rinjaye da ƙananan ƙabilu a ƙasar.

  4. Babu wanda ya mutu a harin da Iran ta kai sansaninmu na Qatar - Amurka

    Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce babu wanda ya mutu a harin da Iran ta kai sansanin sojinta na Al-Udeid da ke Qatar.

    Amurkan ta ce Iran ta kai wa sansanin hari da matsakaitan makamai.

    Shugaba Trump da manyan jami'an Amurka suna wani taro a fadar White House a lokacin da aka kai harin.

    Rahotanni sun ce Iran ta sanar da Qatar kafin ƙaddamar da harin, lamarin da ya bai wa ƙasar damar rufe filayen jiragen samanta.

  5. Iran ta ce Amurka ta kai wa hari ba Qatar ba

    Majalisar tsaron Iran ta ce harin da ta kai sansanonin sojin Amurka da ke cikin Qatar ba shi da niyyar cutar da ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da majalisar ta fitar, ta ce Iran za ta ci gaba da martaba dangantar tarihin da ke tsakaninta da Qatar.

    ''Harin da muka kai ba ya ɗauke da wani hatsari ga mutanen Qatar, saboda ba ƙasar muka nufa ba'', in ji sanarwar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa ''yawan makamai masu linzamin da aka yi amfani da su a harin sun yi daidai da adadin boma-boman da Amurka ta yi amfani da su a cibiyoyin nukiliyar Iran uku''.

    Gwamnatin Qatar dai ta ce na'urorin kakkaɓo makamanta sun samu nasarar daƙile makaman na Iran.

  6. Abin da ya kamata ku sani kan sansanin sojin Amurka na Al Udeid da ke Qatar

    Sansanin Al Udeid, na wajen Doha, babban birnin Qatar, wanda ya kasance cibiyar rundunar sojin sama Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya, kuma sansanin na ɗauke da dakarun Amurka kusan 8,000.

    Haka kuma akwai sojojin Birtaniya a sansanin , da a wasu lokuta ake kiransa da filin jirgin saman Abu Nakhla.

    Cibiyar ta kasance shalkwatar shirya dabarun yaƙin sojojin Amurka da ke aiki a Iraƙi da sauran ƙasashen yankin Gulf.

    A shekarar 2000 ne Qatar ta bai wa Amurka iko da cibiyar Al Udeid.

    Bayan Amurka ta karɓe ragamar sansanin a 2001, Qatar da Amurka suka amince da wata yarjejeniya a 2002 wadda a hukumance ta tabbatar da zaman sojojin Amurka a Al Udeid.

    A shekarar 2024, kafar yaɗa labaran Amurka ta CNN ta cimma wata yarjejeniya da ta amince da tsawaita zaman dakarun Amurka a Qatar na tsawon shekara 10.

  7. Qatar ta yi 'Allah wadai da kakkausar murya' kan harin Iran kan sansanin sojin Amurka

    Gwamnatin Qatar ta yi allah wadai da babbar murya kan harin da Iran ta kai kan sansanin sojin saman Amurka da ke al-Udeid.

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen ƙasar, Majed al-Ansari, ya wallafa a shafinsa X cewa: "Mun ɗauki wannan a matsayin keta haddin Qatar da sararin samaniyarta da dokokin duniya da kuma yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya''

    Ya ce na'urorin kakkaɓo makamai na ƙasar sun ''samu nasarar daƙile hare-haren na makamai masu linzami'' kuma tuni aka janye dakarun Amurka daga sansanin tun kafin harin.

    Ya ƙara da cewa "an ɗauki duka matakan da suka dace wajen tabbatar da lafiyar tsaron lafiyar dakarun a sansanin, ciki har da sojojin Qatar, da dakawarun ƙawance da sauransu''.

    "Mun tabbatar da cewa babau wanda ya rasa rai ko jikkata a harin.''

    Kakain ya ce Qatar na da damar mayar da matarni '' domin rama daidai da abin da aka yi mata''.

  8. Iran ta ce duk wanda ya kai mata hari sai ta ''mayar da martani''

    Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da wata sanarwa jim kaɗan bayan kai wa sansanonin sojin Amurka da ke Qatar da Iraƙi hare-hare.

    Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ambato sanarwar da ke cewa saƙon Iran ga Amurka da ƙawayenta ''a bayyane yake''.

    ''Iran ba za ta yarda da duk wani hari da aka kai cikinta domin keta mutuncinta da kimarta da tsaron ƙasarta a yafi a banza a kowane irin yanayi ba,'' in ji sanarwar dakarin na juyin juya hali.

  9. Labarai da dumi-dumi, 'Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da ke Qatar da Iraƙi'

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta fara abin da ta kira martani mafi girma da nasara kan hare-haren Amurka a cikin ƙasar.

    Kamfanin dillancin labaran ƙasar na Tasnim ya ce dakarun juyin juya halin ƙasar sun ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka da ke Qatar da Iraƙi

    A ƴan mintunan da suka wuce ne aka samu labaran jin ƙarar abubuwan fashewar a Qatar.

    Za mu ci gaba da kwo muku ƙarin bayani kan wannan labari...

  10. Labarai da dumi-dumi, An samu rahotonnin abubuwan fashewa a Qatar

    Kamfanonin dillancin labaran Reuters da AFP sun bayar da rahotonnin jin ƙarar abubuwan fashewa a birnin Doha na Qatar.

    Hakan na zuwa ne bayan samun rahotonin da ke nuna cewa Iran na shirin kai wa sansanonin sojin Amurka da ke Qatar hare-haren makamai masu linzami.

    BBC ta fahimci cewa akwai "barazana mai ƙarfi" ga cibiyar ƙawancen soji da Amurka ke jagoranta a Al-Udeid da ke Qatar.

    Tun da farko an bayar da rahoton cewa ƙasar ta rufe sararin samaniyarta na wucin gadi, inda ta ce sansanonin dakarun sojin ƙasa na cikin shirin ko-ta-kwana.

    Al-Udeid wani babban sansani soji ne da ke wajen Doha, babban birnin Qatar, wanda ya kasance babbar cibiyar rundunar sojin saman Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

  11. Gwamnatin Syria ta ɗauki alƙawarin hukunta waɗanda suka kai hari a Coci

    Shugaban riƙon ƙwarya na Syria, Ahmed Al-Sharaa ya yi alƙawarin hukunta duk masu hannu a harin da aka kai wa wani coci, ranar Lahadi a birnin Damascus.

    Aƙalla mutum 25 aka kashe a harin, wanda aka alaƙanta da ƙungiyar IS.

    Shi ne dai hari na farko irinsa, da aka kai Syria tun bayan hamɓarar da gwamnatin shugaba Bashar al Assad.

    Mr Al-Sharaa, wanda tsohon mai iƙirarin jihadi ne, ya sha alwashin samar da kariya ga mabiya addinai da sauran ƙabilu marasa rinjaye a ƙasar, wanda hakan ya sa ake ganin wannan harin zai zama koma-baya ga gwamnatinsa.

  12. Babu wata hujja da za ta sa a kai wa Iran hari - Putin

    An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin da ministan harkokin waje na Iran Abbas Agarachi a fadar Kremlin da ke birnin Moscow.

    A jawabin da ya gabatar a farkon tattaunawar wanda aka yada a gidan talabijin na gwamnatin Rasha, shugaba Putin ya ce: "Babu wata hujja ko dalili da zai sa a kai wa Iran farmaki."

    Ya ƙara da cewa "na ji daɗin zuwan ka Moscow a yau. Wannan zai ba mu damar tattauna waɗannan batutuwa masu wahala da kuma hanyar shawo kan lamarin."

    Ministan harkokin wajen na Iran ya ce ƙasarsa na da "ƙawance ta ƙut da ƙut" da Rasha.

    Ya ce hare-haren da Isra'ila da Amurka suka kai wa Iran "sun saɓa wa dokoki da ƙa'idojin ƙasa da ƙasa".

    A farkon shekarar nan Iran da Rasha sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna.

    Sai da ba ta haɗa da ƙawancen soji ba kuma ba ta buƙaci Rasha ta kai wa Iran ɗaukin kariya ba.

  13. Isra'ila ta kai hari gidan yarin Evin da ake tsare da ƴansiyasa

    Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare masu tsanani akan birnin Iran.

    Inda aka yi wa ɓarna sun haɗa da gidan yarin Evin, da ake riƙe da fursunonin siyasa.

    A Isra'ila kuma, hare-haren Iran na makamai masu linzami sun yi ɓarna bayan cin ƙarfin na'urorin kakkaɓe makamai na sararin samaniya.

    Hare-haren sun lalata tashar lantarki ta Ashdod, lamarin da ya haifar da katsewar lantarki a gidaje da dama.

  14. Yadda Iran da Isra'ila ke musayar wuta tun da asubahin yau Litinin

    Ƙasashen Isra'ila da Iran na cigaba da ɓarin wuta a tsakaninsu.

    A Isra'ila:

    • Iran ta ƙaddamar da hare-hare ta sama a Isra'ila
    • Kimanin mutum 8,000 ne suka faɗa cikin duhu a kudancin Isra'ila bayan cibiyar makamashin ƙasar ta tabbatar da lalacewar lantarki saboda harin Iran
    • Ba a samu labarin mutuwa

    A Iran

    • Isra'ila ta ƙara zafafa hare-harenta a Iran, waɗanda ministan tsaron Isra'ila Katz ya ce suna yi da "ƙarfinsu."
    • Katz ya ce suna mayar da martani ne ga gwamnatin Iran
    • Rundunar sojin Iran ta yi barazanar mayar da martani "mai tsanani" kan Amurka bayan Trump ya kai hari a cibiyoyin nukiliyar ƙasar.
    • Ana kuma fargabar Iran za ta datse mashigar Hormuz, wadda ke da matuƙar muhimmanci ga dakon makamashi a duniya.
  15. 'Aƙalla mutum 500 hare-haren Isra'ila suka kashe a Iran'

    Kimanin mutum 500 ne suka mutu tun bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran a ranar 13 ga Yuni, bisa cewar ma’aikatar lafiyar ƙasar kamar yadda gidan talabijin na gwamnatin Iran ya bayar da rahoto.

    Rahoton ya ƙara da cewa sama da mutum 3,000 ne suka jikkata.

    Wata ƙungiyar kare haƙkin ɗan adam na Iran da ke bibiyar rikicin ta ce adadin waɗanda suka mutu ya kusan ninki biyu fiye da na gwamnatin.

  16. 'Tankoki uku na man fetur sun ƙauracewa mashigar Hormuz'

    Tankoki uku na dakon man fetur da sinadarai sun canza hanya daga mashigar Hormuz, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito game da harkokin sufurin jiragen ruwa.

    Tankokin sun haɗa da Marie C da Red Ruby, waɗanda yanzu suka tsaya da jiragen su a gaɓar tekun Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE).

    Mashigar Hormuz na ɗaya daga cikin manyan hanyoyin jigilar mai mafi yawa a duniya – kuma akwai hasashen cewa Iran na iya datse ta a matsayin ramuwar gayya dangane da hare-haren da aka yi a cikin ƙasarta.

  17. 'Faransa na adawa da duk wani yunƙurin kifar da gwamnati a Iran'

    Ministan harkokin wajen Faransa ya ce ƙasarsu ba ta goyon bayan kowanne yunƙuri na tilasta kifar da gwamnati a Iran.

    Jean-Noel Barrot ne ya bayyana haka kafin taron ministocin harkokin wajen ƙungiyar Tarayyar Turai da aka gudanar a birnin Brussels.

    Ya ce Iran kaɗai ce za ta iya yanke irin wannan hukunci, yana mai cewa bai kamata a yi tunanin cewa za a iya tilasta kifar da gwamnati da bama-bamai.

    A baya dai, Shugaba Donald Trump ya ambato yiwuwar kifar da gwamnatin Iran.

  18. Kalli yadda hare-haren Iran suka faɗa kusa da tashar samar da wutar lantarkin Israila a Ashdod

  19. Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji a Colombia

    Sojojin ƙasar Colombia sun ce yanzu haka fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a yankin Micay da ke kudu maso yammacin kasar.

    A wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafukan sada zumunta, ta ce an yi garkuwa da sojoji 31 ​​a ranar Asabar yayin da sauran aka ɗauke su jiya Lahadi.

    Sojojin sun ce fararen hular na ɗaukar wannan mataki ne sakamakon matsin lamba da suke fuskanta daga ƴan tawayen kungiyar FARC da ke yankin.

    Yankin na ɗaya daga cikin yankunan da gwamnatin Colombia ke ci gaba da artabu da wasu tsirarun ƴan tawaye na ƙungiyar FARC da ke tayar da ƙayar baya tun bayan da akasarin ƙan kungiyar suka ajiye makamansu a shekara ta 2017.

  20. Amurka ta buƙaci China ta dakatar da Iran daga rufe mashigar Hormuz

    Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya bukaci China da ta dakatar da Iran daga rufe mashigar Hormuz, wanda ke da matuƙar muhimmanci ga sufurin man fetur na duniya.

    Rubio ya yi wannan kira ne bayan rahotanni daga gidan talabijin na gwamnati a Iran sun bayyana cewa majalisar dokokin ƙasar ta amince da wani shiri na rufe mashigar, kodayake hukuncin ƙarshe yana hannun majalisar tsaron ƙasa ta Iran.

    Ya ce rufe mashigiar zai yi wa tattalin arzikin ƙasashe wanda zai fi shafar China, wacce ke sayen mafi yawan man fetur daga Iran,kuma suna da alaƙa me ƙarfi da Tehran.

    Ya kuma gargaɗi cewa hakan zai shafi tattalin arziƙin sauran ƙasashe fiye da na Amurka.

    Kusan kashi 20 na man da duniya ke amfani da shi na wucewa ta mashigin Hormuz, kuma duk wani yunkuri na dakile harkokin sufuri a nan na iya janyo tashin farashin mai a duniya.