Tsananin sanyi ya kashe jarirai shida cikin mako biyu a Gaza - Jami'an lafiya

Asalin hoton, Reuters
Jami'an lafiya a Gaza sun ce an kashe akalla jarirai sabbin haihuwa shida a cikin mako biyu da suka wuce saboda tsananin sanyin da ake fama da shi.
Jami'an lafiya a Gaza sun shaida wa BBC cewar rashin abin dumama jiki ne ya haddasa mutuwar jariran yayin da Falasdinawa ke neman wajen fakewa daga azabar sanyin da ake fama da shi a yankin da suke zaune a cikin tantuna da gidajensu da aka lalata.
Haka kuma jami'an lafiyar sun yi kira ga masu shiga tsakanin na kasa da kasa da su kara kaimi wajen ganin an tabbatar da samar da gidajen tafi da gidanka ga al'ummar ta Gaza.
Har yanzu dai ana nuna rashin tabbas kan ko yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas za ta ci gaba da aiki.

















