Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 16 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Mohammed

  1. Wanda ake zargi da kisan Bondi ya bayyana a kotun majistare a karon farko

    Mutumin da ake zargi da kai harin wurin shakatawar nan na bakin ruwa da ake kira Bondi Beach a Ostraliya Naveed Akram, ya bayyana ta hanyar bidiyo a wata kotun majistare a karon farko.

    Yana fuskantar tuhume-tuhume hamsin da tara kan kisan gillar da ake zargin ya yi wa wasu Yahudawa a birnin Sydney, sama da watanni biyu da suka gabata.

    Mutane 15 ne suka mutu, wasu da dama kuma sun jikkata yayin harin.

    'Yan sanda sun kashe mahaifinsa Sajid Akram a lokacin wani hare harbe.

    A wajen kotun, lauyansa ya ce lokaci bai yi ba da za a iya cewa wanda yake karewa zai amsa laifinsa. Za a ci gaba da sauraron karar a watan Afrilu.

  2. An yi gargaɗi kan samun ƙaruwar raunuka a rikicin Sudan ta Kudu

    Ofishin kula da ayyukan jin ƙai na Majalisar Dinkin Duniya ya ce mutane da dama na samun kulawar likita saboda raunukan da suka samu sakamakon rikici a asibitin Akobo da ke Jihar Jonglei State a ƙasar Sudan ta Kudu bayan sake ɓarkewar faɗa tsakanin ɓangarori masu gaba da juna.

    A cikin sanarwar da ya fitar, ofishin ya ce abokan hulɗarsa na ayyukan jin ƙai na kula da marasa lafiya da suka jikkata a sabbin arangama tsakanin rundunar sojin Sudan ta Kudu da kuma ƙungiyar adawa ta SPLA-IO a yankin Akobo na arewacin Jonglei.

    Ofishin ya yi gargaɗin cewa da dama daga cikin waɗanda suka jikkata suna cikin mawuyacin hali saboda rashin tabbas wajen samun tura su cibiyoyin gaggawa da kuma rashin kulawar ceton rai.

    Ofishin ya kuma bayyana cewa tashin hankali da hare-haren sama da aka ruwaito a Jonglei sun tilasta wa kimanin mutum 280,000 barin muhallansu.

    Wannan gudun hijira ta ƙara tsananta buƙatun agajin jin ƙai a yankunan da abin ya shafa.

    Haka kuma ya ce an sace kayayyakin cibiyoyin lafiya guda 12 tare da lalata wasu, abin da ya kawo cikas ga muhimman ayyukan kiwon lafiya tare da rage damar samar da kulawa ga al’umma masu rauni.

  3. Wace ƙungiya ce Miyetti Allah, wadda Amurka ke zargi kan ayyukan rashin tsaro a Najeriya?

    A cikin makon da ya gabata ne ƴan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da wani ƙudiri a zauren majalisar wanda ya ƙunshi rahoto kan kwamitin bincike game da zargin cin zarafin Kiristoci da musguna musu a Najeriya.

    Ɗan Majalisa Riley Moore da takwaran aikinsa Chris Smith ne suka jagoranci gabatar da ƙudurin, inda suka ce kwamitinsu ya gano abubuwa da dama da suka nuna cewa "an daɗe ana musguna wa Kiristoci a Najeriya".

    Ƴanmajalisar waɗanda na jam'iyyar Republican ne sun nemi Amurka ta sanya takunkumai kan wasu kungiyoyi, da kuma ɗaiɗaikun ƴan Najeriya saboda zargin da hannu a kisan Kiristoci.

    Sauran matakan da ƙudurin ke son a ɗauka su ne hana waɗanda ake zargi da hannu a 'cin zarafin' kiristoci shiga Amurka da riƙe kadarorinsu.

    Cikin waɗanda sunansu ya fito ɓaro-ɓaro a ƙudirin akwai ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore da Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da kuma abin da ƙudurin ya kira "ƙungiyoyin Fulani masu ɗauke da makamai a Najeriya."

  4. Yau El-Rufai zai amsa gayyatar EFCC

    A yau ne ake sa ran tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai zai amsa gayyatar EFCC inda zai bayyana a ofishinta da misalin karfe 10 na safe, kamar yadda ya shaida wa BBC a wata hira da tayi da shi.

    El-Rufai ya bayyana a ranar Juma’ar da ta gabata cewa hukumar ta aike masa da takardar gayyata zuwa ofishinta, kuma ya amince zai je ofisihin a yau Litinin.

    Lamarin na zuwa ne bayan rahotannin da suka ce jami’an tsaro sun ƙwace fasfonsa a Filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe jim kaɗan bayan dawowarsa daga Masar.

    Da yake ƙarin bayani kan wani bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta, El-Rufai ya ce ba shi ne ya yi musayar kalamai da jami’an DSS ba, sai dai su ne suka tare shi a filin jirgi suka buƙaci ya bi su ofishinsu.

    Ya ƙara da cewa babu wata doka a Najeriya ko ƙundin tsarin mulki da ta ba da damar a tare mutum ba tare da takardar gayyata ko sammaci ba.

    Tsohon gwamnan, wanda ke cikin jagororin adawa a jam’iyyar ADC da ke shirin ƙalubalantar shugaban kasa Bola Tinubu na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, ya zargi gwamnati da matsin lamba kan ‘yan adawa ta hanyar kama su da sunan binciken rashawa.

    Ya kuma ce an riga an kama kusan mutane huɗu da suka yi aiki tare da su a Jihar Kaduna, yana mai cewa yana ganin lokaci ne kawai kafin a gayyace shi, abin da yanzu ya tabbata yayin da ake sa ran zai bayyana a gaban EFCC a yau domin amsa tambayoyi.

  5. Netanyahu ya buƙaci a kwashe dukkan uranium ɗin Iran kafin yarjejeniyar nukiliya

    Firaiministan Isra'ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya da ƙasar.

    Benjamin Netanyahu ya faɗi hakan ne yayin da ministan harkokin wajen Iran ya kama hanyar zuwa Switzerland don tattaunawa kai tsaye da Amurka a ranar Talata.

    Tattaunawar za ta ƙunshi manzon musamman na shugaba Trump Steve Witkoff da surukin Shugaban Jared Kushner.

    Tun da farko, mataimakin ministan harkokin wajen Iran ya ce a shirye gwamnatinsu take ta sassauta idan aka ɗage musu takunkumin da aka ƙaƙaba masu.

  6. Yadda Ribadu ya yi martani ga El-Rufai kan zargin shigar da guba Najeriya

    Ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya mayar da martini ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai wanda ya nemi bahasi kan shiga da wata guba mai haɗari cikin ƙasar.

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, ya zargi ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, a ƙaƙashin jagorancin Mallam Nuhu Ribadu, da sayo kimanin kilogiram 10 na wani sinadari mai haɗari da ake kira 'thallium sulphate', daga ƙasar Poland.

    El-Rufai ya yi wannan zargin ne a cikin wata wasiƙa da ya aike wa ofishin Ribadu, wadda kuma ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce jagororin adawar ƙasar na neman ƙarin haske game da wannan batun.

    Saƙon na shi ya ce "Sinadarin thallium na da matuƙar haɗari kuma sinadari ne da ba kasafai ake samunsa ba''.

    Ya ce ya aike da wasiƙar ne domin ya nemi cikakkun bayanai kan yadda aka sayo sinadarin, yayin da ya nuna barazanar da irin wannan sinadari ka iya yi kan lafiyar al'umma.

  7. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.