Duniya ta manta da yaƙin basasar Sudan - MDD
Shugaban hukumar kare haƙƙin ɗan'adam ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce duniya ta manta da yaƙin basasar da ake yi a Sudan.
Volker Turk ya ce akwai buƙatar ɗaukar matakin da ya dace domin kawo ƙarshen kisan ƙare dangin da ake a can.
Mista Turk, ya shaida wa BBC cewa ana aikata cin zarafi da take haƙƙin ɗan'adam a faɗan da ake tsakanin sojojin ƙasar da kuma mayaƙan RSF.
Ya bayyana ƙawanyar da aka yi wa birnin El Fasher tsawon watanni 18 a matsayin abin tashin hankali.
Mista Turk ya ce akwai buƙatar ƙasashen duniya su matsa wa mayaƙan RSF lamba domin kawo ƙarshen kisan ƙare dangi da fyade da ɓatan mutanen da ake gani a Sudan.