Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 18/07/2025

Wannan shafi ne da ke kawo labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Juma'a 18/07/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi da Abdullahi Bello Diginza

  1. Za a gudanar da taron addu'o'i ga Buhari a masallacin ƙasa na Abuja

    Nan gaba a yau ne gwamnatin Najeriya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i ga tsohon shugaban ƙasar, Marigayi Muhammadu Buhari a babban masallacin Juma'a na ƙasa da ke Abuja.

    Fadar shugaban ƙasar ce ta shirya taron domin addu'o'in neman gafara wa tshon shugaban ƙasar.

    Ana sa ran manyan jami'an gwamnati za su halarci taron addu'o'in.

    A ranar Alhamis ne aka gudanar da taron addu'o'i da karramawa da musamman ga tsohon shugaban ƙasar a fadar gwamnatin ƙasar.

  2. Gwamnatin Filato ta zargi jami'an tsaro da rashin kama maharan jihar

    Gwamnatin jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ta zargi jami'an sojojin ƙasar da sakaci wajen rashin kama maharan da suka kashe mutum 27 a garin Tahoss na yankin ƙaramar hukumar Riyom.

    A farkon makon nan ne wasu mahara ɗauke da makamai suka auka wa garin tare da halaka mutum 27 da raunata wasu.

    Yayin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma'a ta cikin shirin ''The Morning Brief'' kwamishiniyar yaɗa labaran jihar, Joyce Ramnap ta ce sojojin da ke yankin sun nuna sakaci wajen rashin kama ko da mutum guda cikin maharan, duk kuwa da kasancewar sojojin a kusa da garin.

    Kwamishiniyar ta ce garin da aka kai harin na kusa da shingen binciken ababen hawa da sojoji ke gudanarwa.

    “Akwai shingen binciken ababen hawa na sojoji, wanda bai fi tazarar mita 200 daga wurin da lamarin ya faru, kuma daga bayanan da muka samu ba wanda suka kama, kuma ba su kashe kowa ba''.

    “Garin nan ba wani gari ba ne mai nisa da za a ce kafin a kai inda suke an yi musu lahani, suna kusa da titi,'' in ji ta.

  3. EU ta amince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

    Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha ƙarin takunkumai saboda yaƙin da take yi da Ukraine.

    Sabbin takunkuman sun shafi fannonin kuɗi da makamashin ƙasar.

    Ƙungiyar ta amince ta ƙaddaye farashin man fetur na Rasha kan sama da dala 40 kawai kan kowace ganga.

    Shugabar hukumar gudanarwar ƙungiyar, Ursula von der Leyen, ta ce EU ƙoƙarin gurgunta babban abin da Rasha ta dogara da shi a yaƙin.

    Ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noel Barrot za su yi abin da zai tilasta wa Rasha tsagaita wuta ba tare da amfani da ƙarfi ba.

    Shugaban Ukraine, Volodymir Zelensky ya yaba wa sabbin takunkuman waɗanda ya kira ''masu muhimmanci da aka aitawar a lokacin da ya dace''.

  4. Gomman makarantun Indiya na fuskantar barazanar tashin boma-bomai

    Gomman makarantu a Indiya sun fuskanci barazanar bom, lamarin da ya tilasta kwashe ɗalibai yayin da ƴansanda ke ci gaba da bincike a makarantun.

    Fiye da makarantu 20 ne a Delhi da wasu 40 a birnin Bangalore suka samu saƙonnin imel da ke cewa an dasa abubuwan fashewa a baƙar leda a makarantun da azuzuwan ɗalibai.

    Kawo yanzu dai ba a samu bom ɗin ko da a makaranta guda ba, to amma suna fuskantar kiɗimewa, yayin da jami'ai ke ci gaba da nema.

    A makonnin baya-bayan nan an samu irin wannan barazana a biranen Delhi da Kolkata.

  5. Hotunan taron addu'ar da aka yi wa Buhari a Villa

    A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga marigayi shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari a taron majalisar zartaswa da ake gudanarwa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

  6. Rasha barazana ce ga duka ƙasashen Turai - Jamus

    Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa Rasha barazana ce ga Turai baki ɗaya ba Ukraine kaɗai ba.

    Mista Merz ya yi gargaɗin cewa, Moscow na tasiri a lamuran da suka shafi zaman lafiya da yanci kai da tsarin siyasar Turai.

    Mista Merz ya ce shi da shugaba Trump suna aiki tare domin kawo ƙarshen yaƙin Ukraine.

    Shugaban gwamnatin ta kuma sake nanata kalaman cewa ƙasashen Turai na buƙatar su iya kare kansu a kodayaushe.

    Ya ce a a halin da ake ciki yanzu gwamnatin Jamus ta soma kashe makudan kuɗaɗe wajen inganta ɓangaren tsaron ƙasarta.

  7. Tinubu zai je Kano ta'aziyyar Dantata

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau Juma'a 18 ga watan Yuli, domin ta'aziyyar rasuwar hamshaƙin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aminu Ɗantata da ya rasu a ƙarshen watan da ya gabata.

    Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce a lokacin da aka yi rasuwar Tinubu ba ya ƙasa, amma duk da haka ya aika tawaga ƙarƙashin ministan tsaron ƙasar domin wakiltarsa a wajen jana'izar.

    Tinubu zai kai ziyarar ta'aziyyra ne ga gwamnatin Kano da kuma iyalan marigayin.

    Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana ziyarar a matsayin mutuntawa ga al'ummar Kano da nuna haɗin kan ƙasa, da kuma martaba abubuwan da marigayin ya aikata.

    Cikin wata sanarwa da gwamnatin Kanon ta fitar, gwamnan ya yi kira ga mazauna jihar su fito domin tarbar shugaban ƙasar bisa tsarin al'adun mutanen Kano.

    A ƙarshen watan da ya gabata ne fitaccen ɗan kasuwar ya rasu a wani asibiti a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, aka kuma binne shi a birnin Madina na ƙasar Saudiyya.

  8. Ba ma goyon bayan hare-haren Isra'ila a Syria - Amurka

    Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da Isra’ila ta kai a Syria a cikin wannan makon.

    Isra'ila dai ta yi ruwan bama-bamai a babban birnin Damascus da kuma lardin Sweida da ke kudancin kasar, inda suka sake kai hare-haren da yammacin jiya Alhamis.

    Ba kasafai ne ake ganin irin wannan rashin jituwa tsakanin Isra’ila da Amurka a ƙarƙashin gwamnatin Trump ba.

    Ba a dai tabbatar da ko Shugaba Trump ya nuna ɓacin ransa kan hare-haren a tattaunawar tarho da suka yi da Firaminista Netanyahu a jiya Alhamis ba.

  9. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa ka-tsaye barkanmu da safiya wannan rana ta Juma'a.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku kasance da mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.