Amurka za ta janye dakarunta 5,000 daga Jamus
Amurka ta ce za ta janye sojojinta 5,00 daga Jamus sakamakon saɓanin da ke ƙaruwa tsakanin ƙasashen biyu.
A baya-bayan nan an samu saɓa i tsakanin Shugaba Trump da shugaban gwamnatin Jamus, Friedrich Merz kan batun yaƙin Iran.
Ma'aikatar tsaron AMurka ta ce za a kwashe sojojin ne cikin wata shida zuwa 12 masu zuwa.
Shugaba Trump ya soki Mista Merz da sauran shugaban ƙasashen ƙungiyar Nato kan ƙin tura sojojinsu domin buɗe mashigar Hormuz.
A ranar Litinin ne shugaban gwamnatin Jmaus ɗin ya ce shugabancin Iran na kunyata Amurka ta hanya sa wakilan Amurak su tashi takanas har Pakistan, domin tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin amma su koma ba tare da wani sakamako ba.
A cikin wannan mako ne dai Mista Trump ya sanar da janye wasu sojojin ƙasarsa daga ƙasashen Italiya da Sifaniya saboda yaƙin na Iran