Cambodia ke saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta - Thailand
Thailand ta zargi Cambodia da saɓa yarjejeniya tsagaita wuta da aka amince bayan kwana biyar na rikicin kan iyaka tsakaninsu.
Thailand ta ce Cambodia ta kai hare-hare wurare da dama jim kaɗan bayan yarjejeniyar tsagaita wutar ta fara aiki, wanda ya sa sojojin Thailand suka mayar da martani.
An bayar da rahoton cewa kura ta lafa a yanzu, amma an dage tattaunawar da ya kamata kwamandojin soji su yi.
A jiya Litinin ne aka amince da yarjejeniyar tsakanin Thailand da Cambodia a tattaunawar da Malasia ta jagoranta