Hare-haren Iran sun lalata tashar lantarkin Kuwait
Ƙasar Kuwait ta ce hare-hare ta sama da Iran ta kai ƙasar ya lalata tashar samar da wutar lantari da kuma cibiyoyin ruwa a ƙasar.
Tehran ta ce ta kai hare-haren ne a matsayin martanin munanan hare-haren da Amurka ta kai kan gadoji biyar da hanyoyin sufurin jiragen ƙasa da kuma filin jirgi cikin dare.
Iran ta kuma ce ta kai hare-haren kan sansanonin sojin Amurka da ke ƙasashen Kuwait da Bahrain da Jordan da kuma Siriya.
Idan har hakan ta tabbata, zai zama karon farko da Iran ta kai babban hari Siriya ƙarƙashin mulkin shugaba Ahmed al-Sharaa, wanda ke ƙoƙarin ganin Siriya ba ta shiga cikin rikicin ba.