Watakila Osimhen ba zai buga wa Najeriya karawa da Afirka ta Kudu ba
Super Eagles za ta fuskanci Afirka ta Kudu ba tare da Victor Osimhen ba a wasan neman shiga gasar cin kofin duniya ranar Talata, saboda raunin da ya ji kamar yadda aka sanar ranar Litinin.
Osimhen ya ji rauni ranar Asabar a lokacin da yake buga wa Najeriya karawar da ta doke Rwanda 1-0 a Uyo, yanzu ba zai samu buga fafatawar da za a yi a Blomfontein ba.
Afirka ta Kudu tana jan ragama a rukuni na uku da tazarar maki shida tsakaninta da Najeriya, koda yake ana sa ran Fifa za ta rage maki uku daga na Afirka ta Kudu, saboda amfani da ɗan wasan da bai cika ka'ida ba.
Duk wadda ta ja ragamar rukunin ita ce za ta wakilci Afirka daga taran da ake sa ran za su je gasar cin kofin duniya daga nahiyar da za a yi a 2026 a Amurka da Mexico da kuma Canada.