Adadin mutanen da ambaliya ta kashe a jihar Neja ya kai 230
Adadin mutanen da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a jihar Neja sun ƙaru zuwa 230 yayin da har yanzu ake neman sama da mutum 400, a cewar Mataimakin shugban ƙaramar hukumar Mokwa, Musa Kimboku.
A makon da ya gabata ne ambaliyar, wadda ruwan sama mai ƙarfin gaske ya haifar, ta ɗaiɗaita ɗaruruwan gidaje da mazauna cikinsu.
Mataimakin shugban ƙaramar hukumar ya faɗa wa BBC cewa ana ci gaba da aikin tona ƙasa domin neman mutanen da ake tunanin ƙasa ta binne su.
Ya ce hakan ya taimaka wajen rage warin da yake tashi a yankin saboda gawarwaki.
Ana kallon ambaliyar a matsayin mafi muni cikin shekara 50 da aka taɓa gani a Najeriya, wadda ta zarta ta birnin Maiduguri a watan Satumban 2024.