Amurka da Isra'ila sun ce suna shirin shiga sabon mataki a yaƙin Iran
Amurka da Isra'ila sun ce suna shirin shiga sabon mataki na gaba a yakin da suke yi da Iran
Sakataren tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya ce, suna dab da kara karfin hare-haren da suke kai wa Iran din sosai.
Rundunar sojin Isra'ila kuma ta ce, ta fara, kai abin da ta kira manyan hare-hare a kan cibiyoyi da kayayyaki a Tehran, babban birnin Iran din.
Shugaban babbar rundunar sojin Amurka, ya ce an kassara duk wani karfi na amfani da kai hari da makamai masu linzami na Iran, na yanzu da kuma na nan gaba.
Admiral Brad Cooper ya kuma ce Amurka ta nutsar da jiragen sojin ruwa na Iran sama da talatin.