Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/09/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Aisha Babangida

  1. Ana ce-ce-ku-ce kan shawarar Trump na mata masu ciki su daina amfani da paracetamol

    Ana ci gaba da sukar shawarar da shugaban Amurka, Donald Trump ya bayar akan daina amfani da kwayar paracetamol ga mace mai dauke da juna biyu saboda haɗarin haihuwar jariri mai lalurar Autism .

    Gidauniyar kula da masu lalurar Autism ta ce ta damu matuka, sannan kuma ta bayyana cewa babu wani ingantaccen bincike na kimiyya da ya danganta alakar maganin da lalurar Autism.

    Trump ya ce ya bayar da shawararce saboda ana samun ƙaruwar masu lalurar Autism, kuma yana ganin kamar maganin na da alaka da hakan.

    Da ya ke jawabi a fadar white house tare da sakataren kula da harkokin lafiya na kasar Robert F Kennedy, shugaban ya kuma soki wasu alluran rigakafin da ake yi wa yara inda ya ce wasunsu na janyowa yara kamuwa da cutuka masu matukar hadari.

    Mahukunta a ɓangaren lafiya a kasar za su yi nazari akan wanann shawara inda za su zabi ko su yi amfani da shawarar shugaban kasar ko kuma a'a.

  2. Falasɗinu ta buƙaci sauran ƙasashe su amince da ƙasar Falasɗinu

    Shugaban Falasdinawa ya yi kira da a samu karin wasu kasashe da za su bi bayan Faransa da Birtaniya wajen amincewa da Falasɗinu a matsayin kasa.

    Shugaban Falasɗinawan ya cewa "mun yaba wa matsayin ƙasashen da suka amince da Falasɗinu a matsayin kasa, sannan kuma muna kira ga wadanda ba su bayyana matsayarsu ba da su bi sahun wadannan kasashe."

    Mahmud Abbas, ya kuma jinjina wa shugaban Faransa Emmanuel Macron, a taron Majalisar Dinkin Duniya cewa duk wata hanyar samun zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya ta dogara ne wajen samar da kasashe biyu masu 'yanci.

    Ana kyautata tsammanin shugaba Trump zai mayar da martani akan wannan mataki na wadanann ƙasashe a ganawar da zai yi da shugabannin kasashen Larabawa da kuma jagororin addinin musulunci a New York.

  3. Mali da Nijar da Burkin Faso sun fice daga kotun hukunta manyan laifuka ta ICC

    Ƙasashen yankin sahel uku, Mali da Nijar a Burkina Faso a cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa da ke ɗauke da sa hanun shugaban gwamnatin mulkin sojin ƙasar Mali, Janar Assimi Goita, sun sanar da ficewa daga ICC, inda suka zargi kotun ta hukunta manyan laifuka ta duniya da rashin adalci da kuma cewa ta gaza wajan yanke hukunci kan munanan laifukan da aka aikata a duniya

    Wannan mataki dai shi ne na baya-baya nan da ƙasashen da ke ƙarƙashin muljin soji suka ɗauka tun bayan ɓallewarsu daga ƙungiyar ECOWAS inda daga bisani suka kafa tasu ƙungiya da ake kira AES wato Allinace for Sahel States.

    Ƙasashen uku sun ƙuduri aniyar ƙarfafa ƴancinsu ta hanyar komawa ga tsarin zaman lafiya da adalci a cikin gida tare da jajircewa wajan kare haƙƙin bildama da hukunta masu aikata laifi kamar yadda dokokin zamantakewa suka tanada.

    A shekarar 2003 ne aka kafa kotun ta ICC wadda aka ɗaura wa alhakin hukunta laifukan da suka shafi kisan ƙare dangi da cin zarafin biladama da laifukan yaƙi kuma tun lokacin da fara aiki kotun ta ICC ta saurari ƙararraki 33

    Masu sukar kotun ciki har da shugaban ƙasar Rwanda Paul Kagame sun zargi kotun da nuna son zuciya ko rashin adalci saboda ta maida hanakli kan ƙasashen Afrika.

    Ƙasashen yannkin Sahel uku waɗanda a halin yanzu ke fama da rashin tsaro sakamakon hare-haren mayaƙa masu iƙirarnin jihadi sun yanke alaƙa da wasu ƙasashen yamma da suka haɗa da Faransa inda suka ƙulla ƙawance da Rasha domin samun tallafin soji da kuma inganta cinikayya tsakaninsu

  4. Buɗewa

    Jama'a barkanmu safiya, barkanmu da sake haɗuwa da ku a wannan shafin na labaran kai-tsaye daga nan sashen Hausa na BBC Hausa.

    Ku leƙa shafukanmu na sada zumunta irin su Facebook da Instagram da X da ma zaurenmu na Whatsapp domin karanta wasu labaran da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.