Tinubu ya umarci sojoji su canza salo wajen yaƙi da ’yan bindiga a Katsina
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya umarci rundunar sojojin ƙasar da su canza salo wajen fatattakar ƴan bingida a jihar Katsina ta hanyar amfani da na'urori na zamani wajen sanya ido kan matsalar tsaro.
Tinubu bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gwamnan jihar Dikko Radda da wasu shugabannin jihar a fadar gwamnati.
Tinubu ya kuma jaddada muhimancin magance matsalar tsaro a faɗin ƙasar.
"Za a ƙara ɗaukar matakan tsaro na cikin gida, ciki har da yiwuwar kafa ƴan sandan jihohi da ƙarfafa masu gadin daji."
Ya kuma buƙaci a rika samun rahoton aiki kullum daga Katsina.
Shugaban ya ce dole ne a kare rayuka da yara da wuraren ibada da kasuwanci, yana mai cewa: “Ba za mu bari waɗannan ƴan bindigan su tsoratar da mu ba.”