Netanyahu ya zargi Iran da yunƙurin kashe shi
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya zargi Iran da yunƙurin kashe shi da matarsa, bayan harin jirgi maras matuƙin da aka ƙaddamar daga Lebanon zuwa gidan shi.
Mista Netanyahu ya bayyana harin da babban kuskure, tuni kuma ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon da Iran ke mara wa baya ta ɗauki alhakin kai harin.
Bangaren Hezbolla sun ƙara faɗaɗa hare-harensu ba kawai farar hula ba, bangaren Isra'ila abin damuwa ne a kai wa mutum mai daraja ta daya a gwamnati hari.
Tun daga lokacin da aka kai harin, sojojin Isra'ila suka ci gaba da zafafa kai hare-hare ta sama kudancin birnin Beruit, sun ce suna kai harin ne wuraren da mayaƙan Hezbollah ke ɓoye makamai da shalkwatar tsaron sirrin ƙungiyar.