Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 14 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida and Umar Mikail

  1. Ƙasar Benin ta hana fitar da masara zuwa Nijar

    Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron zabbi wanda hukumomi suka ɗora alhakin safarar su zuwa ƙasashen da ke maƙwabtaka da ita, musamman ƙasar Nijar.

    Kamfanin dillancin labaran kasar ya ruwaito cewa wannan na zuwa ne bayan ma’aikatar sufurin jamhuriyar Nijar ta haramtawa motocin ɗaukar kaya da aka yi wa rajista a Benin jigilar kayayyakinsu.

    “Ma’aikatar sufuri da kayan aiki na son sanar da duk masu ruwa da tsaki a harkar sufurin ƙasashen duniya cewa an keɓe tarin kayayyakin da za su je Nijar daga tashar Lome ko kuma a ko’ina a Jamhuriyar Togo ga motocin da aka yi wa rajista a Nijar kaɗai da Togo," in ji sanarwar da aka fitar.

    Nijar dai ta karkatar da akasarin kayayyakin da take shigarwa da su ƙasar Togo, sakamakon yadda alaƙar da ke tsakaninta da ƙasar Benin, mai adawa da gwamnatin mulkin soji da ta hamɓarar da tsohon shugaban ƙasar Mohamed Bazoum, ta taɓarɓare.

    Nijar dai na zargin ƙasar Benin da ɗaukar nauyin sansanonin ƴan ta’adda na kasar Faransa da ke shirin hargitsa yankin Sahel, kamar yadda ta musanta.

    Jamhuriyar Benin ta dakatar da fitar da man fetur a yayin da Nijar ke ci gaba da rufe iyakokinta duk da cewa an ɗage takunkumin da shugabannin kasashen yammacin Afirka suka ƙaƙaba mata kan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Yulin 2023.

  2. Ramaphosa zai rattaɓa hannu kan dokar kiwon lafiya kafin zaɓe

    Shugaban ƙasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa zai rattaɓa hannu a kan wata doka mai cike da cece-kuce kan harkokin kiwon lafiyar ƙasar da ke da nufin samar da wadataccen abinci ga miliyoyin talakawan ƙasar.

    Dokar Inshorar Kiwon Lafiya ta Kasa (NHI) tana neman bai wa 'yan Afirka ta Kudu da suka haɗa da masu arziki ko matalauta damar samun ingantaccen kiwon lafiya.

    ‘Yan majalisa ne suka amince da shi a shekarar da ta gabata kuma ana shirin aiwatar da shi a matakai kan kuɗi biliyoyin daloli.

    Jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin farar hula sun buƙaci a mayar da wannan ƙudiri zuwa majalisar dokokin ƙasar, suna masu cewa yana da kura-kurai a tsarin da ake yi a yanzu.

    A ranar Laraba ne za a rattaɓa hannu kan ƙudirin dokar a ofishin shugaban ƙasa da ke babban birnin ƙasar Pretoria, inji fadar shugaban ƙasar.

    Hakan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan gabanin zaɓen ƙasar da za a gudanar a ranar 29 ga watan Mayu.

  3. Labarai da dumi-dumi, Varane zai bar Manchester United

    Dan kwallon baya na Manchester United, Raphael Varane zai bar kulob din idan kwangilarsa ta kare a karshen kakar wasa ta bana.

    Dan wasan mai shekaru 31, ya koma Old Trafford ne daga Real Madrid a bazarar 2021 a kan fan miliyan 34.

    Varane ya buga wa United wasa sau 93.

    Tsohon dan kwallon Faransa ya taimaka wa United lashe kofin Caraboa a 2023 lokacin da tawagar Erik ten Hag ta doke Newcastle United a wasan karshe.

    "Kowa a United na godiya ga Rapha saboda aiki da yayi kuma muna masa fatan alheri a nan gaba," in ji sanarwar United.

  4. EFCC za ta gurfanar da Emefiele kan sabunta takardun naira

    Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa arzikin Najeriya ta'annati, EFCC za ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin ƙasar, Godwin Emefiele ranar Laraba bisa bayar da izinin buga sabbin takardun naira na miliyan 684.5 a kan naira biliyan 18.96.

    Tun farko an tsara gurfanar da shi ne ranar 30 ga watan Afrilu da ya gabata amma aka ɗage ranar bayan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kotun da kuma ɓangarorin.

    A tuhume-tuhumen huɗu da aka shigar a kansa, EFCC ta yi zargin Emefiele ya yi burus da umarnin kotu da nufin jefa jama'a cikin mawuyacin hali lokacin aiwatar da tsarin sauya takardun naira da gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi.

    EFCC ta kuma zargi Emefiele da ba da izinin cirar naira biliyan 124.9 daga asusun bai ɗaya na ajiyar kuɗaɗen shiga na gwamnati ba bisa ƙa'ida ba.

    Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa tsohon gwamnan CBN zai gurfana a gaban kotu kan waɗannan tuhume-tuhume gaban mai shari'a Maryann Anenih ta babbar kotun tarayya da ke Abuja.

    A ranar 17 ga watan Nuwamban 2023, an gurfanar da Emefiele gaban mai shari'a Hamza Muazu kan tuhume-tuhume shida kan wata badaƙala ta siyan kayayyaki, zargin da ya musanta.

    An kuma zarge shi da yin amfani da matsayinsa wajen amincewa da kwangilar siyan motoci 43 a kan kuɗi naira biliyan 1.2 daga 2018 zuwa 2020.

    A ranar 8 ga watan Afrilun 2014 ne kuma EFCC ta sake gurfanar da Emefiele tare da Henry Omole gaban mai shari'a, Rahman Oshodi na kotun sauraron laifuka na musamman da ke zamanta a Ikeja, jihar Legas kan zargin badaƙalar kuɗi ta dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8.

    Emefiele dai ya musanta yin badaƙalar.

    • Me ya sa ake ƙarancin takardun naira a sassan Najeriya?
    • 'Yan Najeriya na kumfar baki a kan 'ɓacewar sabbin takardun naira'
  5. An rufe ofishin jakadancin Amurka a Tanzaniya saboda katsewar intanet

    An rufe ofishin jakadancin Amurka a Tanzaniya na tsawon kwanaki biyu sakamakon matsalar katsewar intanet da ta addabi wasu ƙasashen gabashin Afirka.

    Ofishin jakadancin a cikin wani sako da ya fitar a kan shafin sada zumunta na X a ranar Litinin ya ce "Saboda lalacewar sabis na hanyar sadarwa a duk fadin kasar, ofishin zai kasance a rufe ga jama'a."

    Ofishin ya soke duk wasu ayyuka na ranar Talata da Laraba tare da sake sanya su zuwa wani lokaci.

    An ci gaba da samun katsewar intanet tun da safiyar Lahadi, lamarin da ya haifar da ƙalubale a hanyar sadarwa a kasashen Tanzania da Kenya da Rwanda da kuma Uganda.

    Ma'auni da ƙungiyar sa ido ta intanet NetBlockson ta nuna ranar Litinin ya nuna cewa ƙasar Tanzaniya ta fi fama da matsalar katsewar.

    Ƙatsewar intanet ɗin ya samo asali ne sakamakon kurakuran da ke wayoyin da ke ƙarƙashin teku da suka haɗa yankin da sauran ƙasashen duniya ta Afirka ta Kudu, kamar yadda masanin masana'antu Ben Roberts ya shaida wa BBC.

    Zuwa ranar Litinin ɗin da ta gabata, wasu ‘yan yankin gabashin Afirka sun ci gaba da samun matsalar intanet inda wasu kamfanonin sadarwa ke nuna cewa har yanzu ba a kai ga warware matsalar ba.

    • Me ya sa ake yawan samun matsalar katsewar intanet?
    • Nijar ta shiga matsalar lantarki bayan katsewa daga Najeriya
  6. Adadin ƴan gudun hijra a duniya ya ƙaru zuwa kusan miliyan 76

    Wata ƙungiya da ke sa ido mutanen da aka ɗaiɗaita a duniya ta ce adadin mutanen da suka ɗaiɗaita a faɗin duniya ya ƙaru zuwa miliyan 75.9 a ƙarshen shekarar da ta gabata - adadin da ba a taɓa gani ba.

    Ƙungiyar ta Internal Displacement Monitoring Center ta ce an sake samun wasu adadin mutane masu yawa da suka tsere daga gidajensu a 2023, musamman a Sudan da jamhuriyar dimokraɗiyyar Kongo da Gaza.

    Ta ƙara da cewa adadin mutanen da suka ɗaiɗaita ya ƙaru da kashi 50 cikin 100 cikin shekaru biyar da suka gabata.

    Duk da cewa galibinsu sun tsere ne saboda yaƙi, ƙarin wasu sun ɗaiɗaita ta hanyar afkuwar bala'i sakamakon sauyin yanayi.

    • Abin da ya sa ba ma so mu koma gida — ‘Yan gudun hijira
    • Yunwa da fyaɗe sun mamaye mutanen da suka tsira daga yaƙin Sudan
  7. Blinken na ziyara a Ukraine yayin da Rasha ke ta kai hare-hare

    Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa birnin Kiev domin wata ziyarar ba-zata.

    Blinken dai ya sauka a babban birnin Ukraine a safiyar yau bayan tafiyar sa'o'i tara.

    Ana sa ran zai gana da shugaban ƙasar Volodymyr Zelensky da sauran jami'ai a yayin ziyarar inda aka ce zai isar da saƙon "tabbaci mai ƙarfi" ga 'yan ƙasar ta Ukraine.

    Ziyarar tasa ta zo ne a daidai lokacin da ƙasar ke kokarin dakile wani gagarumin farmaki da Rasha ta kai a kusa da birnin Kharkiv na biyu mafi girma.

    Zuwan Blinken kuma ya cika makonni uku tun bayan da Majalisar Dokokin Amurka ta amince da wani sabon tallafin dala biliyan 61 ga Ukraine.

    • Abun da ya sa Putin ke samun ƙarfin iko fiye da kowane lokaci
    • Shin Sojojin Ukraine ne ke faɗa da dakarun Wagner a yaƙin Sudan?
  8. Tinubu ya nemi hukumomi su koma amfani da motoci masu amfani da iskar gas

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya umarci duka hukumomin gwamnati da su sayi motoci masu amfani da iskar gas a wani ɓangare na yunƙurin da ƙasar ke yi na komawa amfani da makamashi mara gurɓata muhalli tare da rage tsadar mai.

    Umarnin na ƙunshe cikin sanarwar da kakakin shugaban Ajuri Ngelale ya fitar inda ta ce Mista Tinubu ya ce yana sa ran duka hukumomin gwamnati da ma'aikatu su soma yasar da motocin da suke da su masu amfani man fetur ko dizel.

    Shugaban ya ƙara da cewa duka sabbin motocin gwamnati ko babura masu ƙafa uku dole ne su yi amfani da nau'in iskar gas na CNG da hasken rana ko ta hanyoyin makamashi.

    Shugaban ya kuma bayyana ƙudirinsa na amfani da iskar gas yadda ya kamata domin magance tsadar sufuri ga al'umma.

    Umarnin shugaban ya zo ne ƴan makonni bayan da gwamnati ta sanar da ƙudirinta na samar da motocin bas da babura masu ƙafa uku fiye da 2,000 masu amfani da iskar gas a ƙoƙarin rage tsadar sufuri kafin 29 ga watan Mayu, lokacin da shugaban zai cika shekara ɗaya a karagar mulki.

    • Mene ne tallafin man fetur kuma me ya sa batun cire shi ke kaɗa hantar ƴan Najeriya?
    • Wahalar man fetur: 'Da kuɗinmu ma mun rasa mai tsadar'
  9. 'Allurar rage ƙiba na iya rage haɗarin bugawar zuciya'

    An gano alluran rage ƙiba irin su Ozempic da Wegovy da ke taimakawa wajen rage kamuwa da bugun zuciya da shanyewar ɓarin jiki ko ya girma mutum ko ƙibarsa take.

    Masu bincike sun yi maraba da wannan nazari da suke cewa zai taimaka sosai wajen shawo kan matsalolin rage kitse a jiki.

    A lokacin wani taron manema labarai a birnin Venice, jagoran bincikin, John Deanfield daga jami'ar Landan ya ce za a rage yi wa mutane waɗannan allurai musamman tsakanin waɗanda suka matsu su rage ƙiba.

    Wakiliyar BBC ta ce, masu binciken sun gano cewa akwai wasu sinadarai a waɗannan allurai da ke taimakawa wajen rage barazanar kamuwa da bugun zuciya da daidaita sukari da hawan jini ko da mutum bai rage ƙiba ba a lokacin shan magani.

    • Mene ne ke janyo yawan son cin ƙwalama?
    • Mene ne bijirewar jiki ga sinadarin Insulin?
  10. An sake ɗaiɗaita kashi 20 cikin 100 na al'ummar Gaza – MDD

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce an sake raba kashi 20 cikin 100 na al'ummar Gaza da muhallansu a cikin makonni da suka gabata yayinda Isra'ila ke cigaba da luguden bama-bamai a Rafah.

    Falasɗinawa fararan-hula na ta tserewa daga yankin da ke kudancin Gaza da kuma Arewaci, inda faɗa ke tsananta.

    Majalisar tace umartar mutane su fice daga waɗannan yankuna da kuma hare-haren soji sun sake ta'azzara matsalolin jin-ƙai da kuma mayar da hannun agogo baya.

    Sannan ana sake samun ƙarin yara da ke fama da rashin abinci mai gina jiki.

    Baya ga Rafah da Isra'ila ta tasa a gaba, sansanin Jabalia da ke arewacin Gaza ma bai tsira ba, inda take zargin cewa Hamas na ɓoyewa cikin mutane.

    • Gaza: Ko Isra’ila ta samu biyan bukata bayan wata shida da fara yaki?
    • Ana zargin Isra'ila da laifukan yaƙi bayan kisan yaro Bafalasɗine
  11. Barka da Safiya!

    Muna yi maku barka da war haka, da fatan an wayi gari cikin aminci.

    Da fatan za ku bibiye mu domin sanin halin da duniya ke ciki, musamman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Jamhuriyar Nijar da Kamaru da ma wasu sassan duniya.

    Kuna kuma iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin karanta ƙarin labarai da kallon bidiyo.