Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Usman Minjibir and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Likitoci na ci gaba da yajin aiki a Kenya bayan gaza cimma matsaya da gwamnati

    Tattaunawa tsakanin gwamnatin Kenya da likitoci masu yajin aiki ta gamu da cikas abin da ke ƙara jefa rayuwar ƴan ƙasar da ke neman magani a asibitocin gwamnati cikin garari.

    Yajin aikin da gamayyar ƙungiyar likitoci ta tsunduma tun wata biyu baya kan rashin biyansu kuɗi da gaza ɗaukan likitoci masu neman horo.

    Jami'an ƙungiyar sun gaza halartar wani muhimmin taro ranar Talata wanda shugaban ma'aikatan ƙasar, Felix Koskei ya kira bayan shafe kwanaki ana tattaunawa.

    Bayan taron majalisar zartaswa da shugaba William Ruto ya jagoranta, gwamnati ta ce an biya buƙatun likitocin ban da rashin jituwar da suke da ita game da likitoci masu neman horo.

    Gwamnatin ta ce ba za ta iya biyan likitoci masu neman horo dala 1,500 ba. Ta dage cewa za ta iya biyan dala 520 duk wata ga likitocin.

    Ƙungiyar likitocin ta yi fatali da tayin su koma aiki inda ta ce dole ne a biya likitocin masu neman horo abin da suka nema.

    Mista Koskei ya zargi likitocin da bijirewa umarnin kotu da kuma rashin mutunta yarjeniyoyin da aka cimma yayin taron.

    Likitocin da ke yajin aiki na son gwamnatin Kenya ta inganta walwalarsu da sauran buƙatu.

  2. Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram uku a Kamaru

    Dakarun haɗin gwiwa da ke yaƙar Boko Haram - MNJTF ƙarƙashin rundunar ta ɗaya da ke garin Mora a Kamaru sun kashe mayaƙan Boko Haram uku a sumame daban-daban da suka kai a Zigue da Soueram a ranakun 15 da kuma 22 na watan Afrilun 2024.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar soji, Leftenar Kanar Abubakar Abdullahi ya sanyawa hannu ta ce a harin farkon na ranar 15 ya faru ne a garin Zigue da ke iyakar Kamaru wanda ya yi sanadiyyar kashe ɗan boko haram ɗaya.

    Hari na biyu ya faru a safiyar ranar 22 a garin Soueram da ke kusa da iyakar Kamaru da Najeriya inda dakarun suka yi nasarar kashe wasu mayaƙan Boko Haram guda biyu.

    Yayin sumamen an gano bindigar PKM guda ɗaya da AK-47 ɗaya da alburusai 5 da kuma harsasai guda 20.

    Sanarwar ta ce dakarun sun ci gaba da nuna jin daɗinsu kan yadda mazauna garuruwan ke basu goyon baya da kuma samar masu da bayanai wanda ya taimaka masu wajen cimma nasarorin.

    Ya ce "muna neman al'umomi su ci gaba da bamu goyon baya kuma MNJTF za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro a tafkin Chadi da ƙara ƙarfafa murƙushe ayyukan ta'addanci a yankin".

    • Yadda duniya ta manta da garin Chibok tare da ƴanmatan makaranta ​​da aka sace
  3. An zargi mataimakin ministan tsaron Rasha da karɓar cin hanci

    An zargi mataimakin ministan tsaron Rasha da karɓar cin hanci inda wata kotu ta tsare shi a Moscow.

    Timur Ivanov, wanda ya musanta zrge-zargen, ana tuhumarsa da karɓar cin hanci.

    Mista Ivanov wanda aka naɗa kan muƙamin a 2016, yana da iko ne da kayan aikin sojin Rasha.

    Masu fafutuka sun daɗe suna suka kan zarge-zargen rashawa a Rasha.

    Sai dai ba a cika jin manyan mutane cikin irin wannan badaƙala tun mamayar da Rasha ta yi wa Ukraine a 2022.

    Ana kallon mista Ivanov a matsayin makusancin ministan tsaro, Sergei Shoigu kuma ya yi aiki tare da shi tsawon shekaru. Ya taɓa riƙe muƙamin mataimakin firaiministan Moscow inda Mista Shoigu mulka a matsayin gwamna.

    A 2022, ƙungiyar yaƙi da rashawa ta ACF, da marigayi jagoran ƴan hamayyar ƙasar Alexei Navalny ya kafa, ta zargi Mista Ivanov da hannu a rashawa yayin gudanar da aiki a yankunan Ukraine da Rasha ta mamaye.

    Ƙungiyar ta ce ya amfana daga ayyukan da aka yi a birnin Mariupol, da Rasha ta lalata akasarinsa bayan samamen da aka yi wa Ukraine.

    • An tabbatar da mutuwar zaratan sojojin Rasha dubu 50
  4. Rabi'u Pele, ɗan ƙwallon Kano da ke son buga wa Barca ko Arsenal wasa

  5. An kuɓutar da yaron da ya maƙale a ambaliyar ruwa a Kenya

    Wani jirgin helikwafta na ƴan sandan Kenya ya kuɓutar da yaro ɗan shekara biyar da ambaliyar ruwa ta tafi da shi ranar Talata.

    Mahaifin yaron ya ƙyale shi lokacin da ruwa ya taso sama, kamar yadda ƴan sanda suka bayyana.

    Ƙungiyar kula da jin ƙai ta duniya wadda ta gano inda yaron yake ta hanyar amfani da na'urar drone, ta ankarar da ƴan sanda da suka aika helikwafta daga Nairobi.

    Yunƙurin farko na kuɓutar da yaron a kwale-kwale ya gamu da cikas saboda rashin kyawun yanayi, in ji ƙungiyar agaji ta Red Cross a Kenya.

    "An yi nasarar kuɓutar da yaron, wanda da ka gan shi ya yi matuƙar kaɗuwa da halin da ya shiga an kuma kai shi asibiti da ke kusa domin duba lafiyarsa," in ji ƙungiyar.

    A kwanakin baya-bayan nan, ana mamakon ruwan sama a Kenya da gabashin Afirka abin da ya janyo ambaliyar ruwa da ɓarna.

    A Kenya, ambaliyar ta shafi larduna 23 cikin 47 na ƙasar inda mutane da dama suka maƙale.

    Fiye da mutum 188 aka kuɓutar tun soma ambaliyar kamar yadda Kenya Red Cross ta shaida.

    Ta ƙara da cewa ambaliyar ruwan ta ɗaiɗaita gidaje 11,206 inda kadada 27,716 ta nutse sannan fiye da dabbobi 4,800 sun mutu.

    • Ambaliyar Ghana: ‘Ruwa ya cinye gida da gonata'
  6. Shugabannin duniya na taro a Canada kan illar robobi da leda

    Wakilan kasashen duniya na taro a Canada karo na hudu domin shawo kan matsalar gurɓatar yanayi da robobi da leda ke haifarwa.

    A wajen taron da suka gudanar a sheakarar 2021 ne ƙasashen suka amince cewa za su cimma matsaya zuwa karshen wannan shekarar ta 2024.

    Masu rajin kare muhalli na dora alhakin hakan ga ƙsashen dake da albarkatun mai.

    Wakilin BBC ya ce an samu mabambantan ra'ayoyin kan hanyar da za a shawo kan matsar, inda wasu ke ganin a taƙaita samar da robobi da leda yayin da wasu ke ganin a hana ma'aikatun amfani da wasu sinadarai.

    • Matsalar shara: Shin sake sarrafa leda da roba na yin tasiri?
  7. 'Yansanda a Haiti sun tarwatsa mutanen da suka taru ƙofar gidan Ariel Henry

    Ƴansanda a Haiti sun yi amfani da hayaƙi mai sa hawaye wajen tarwatsa dandazon mutanen da suka yi cincirindo a gaban tsohon gidan shugaban ƙasar gabanin canji gwamnati.

    Rahotannin da ba a tantance ba na cewa za a rantsar da kwamitin mutum tara na shugaban ƙasa na riƙo a gobe Alhamis domin maye gurbin firaiministan ƙasar mai barin gado.

    Majalisar Dinkin duniya ta bayyana halin da ake ciki a ƙasar da mummunan yanayi sakamakon rikicin ƴan daba.

    • Yadda gungun ƴandaba suka mamaye Haiti
  8. Argentina na son a kama ministan cikin gidan Iran, Ahmed Vahidi

    Ƙasar Argentina ta yi kira da a kama ministan cikin gida na Iran, bayan da ta zarge shi da hannu a tashin bam din cibiyar al'adu ta Yahudawa da ke Buwainos Ay-res shekaru 30 da suka gabata.

    A cikin wata sanarwa da ministan harkokin ƙasashen wajen ƙasar ya fitar ya ce ya nemi tallafin kungiyar ƴansandan ƙasa da ƙasa wajen tsare Ahmad Vahidi.

    Tashin bam din da ya kashe mutum tamanin da biyar shi ne hatsari sannan mafi muni da ya taɓa faruwa a Argentina.

    Wannan dai na zuwa ne bayan da Isra'ila da ƙasar Iran suka sanya zare inda suka kai wa juna hare-hare.

    • Ta yaya za a kwatanta ƙarfin Iran da na Isra'ila?
  9. Zelensky na Ukraine ya yi wa Amurka godiya kan tallafin dala biliyan 61

    Shugaba Volodymyr Zelenskyya na Ukraine ya miƙa godiyarsa ga Majalisar Dattawan Amurka da ta amince da abin da ya kira da tallafi mai matuƙar mahimmanci ga Ukraine.

    Ya ce matakin ya ƙara fito da rawar da Amurka ke takawa wajen tabbatar da dimokradiyyya a duniya.

    Zalensky ya ɗaɗ yana nuna cewa Amurkar ta fi damuwa da ƙasar Isra'ila inda yake zargin duniya ta juya masa baya.

    A karshe dai kan 'yan majalisun ya hadu kuma murya ta zo daya inda suka amince da wannan tallafi na dala miliyan dubu 95 ga Ukraine da Isra’ila da kuma Taiwan.

    Daga cikin kudin tallafin dala biliyan 95, akwai dala bliyan 61 ga Ukraine da Shugaba Biden ya ce Ukraine na matukar bukata domin samar da garkuwa ta sama a yakin da kasar ke yi da Rasha.

    • Majalisar Amurka ta amince da tallafin dala biliyan 95 ga Ukraine da Isra'ila
  10. Zan yi murabus idan na gaza kai ƙarshen binciken Yahaya Bello – Shugaban EFCC

    Shugaban hukumar EFCC da ke yaƙi da masu yi wa arzikin Najeriya zagon ƙasa, Ola Olukoyede ya sha alwashin yin murabus idan na gaza gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.

    A wani taron tattaunawa da zaɓaɓɓun editoci a hedikwatar hukumar da ke Abuja, babban birnin Najeriya, shugaban hukumar ya yi alƙawarin hukunta duk masu kawo kawo tarnaƙi ga kama tsohon gwamnan.

    A ranar 18 ga watan Afrilu, EFCC ta ayyana Bello a matsayin wanda take nema ruwa a jallo saboda zarginsa da badaƙalar kuɗi ta naira miliyan 80.

    Yahaya Bello dai bai bayyana gaban kotu ba tun bayan ayyana ana nemansa ruwa a jallo.

    Shugaban EFCC ya ce da kansa ya kira Bello cikin mutunci inda ya nemi da ya bayyana gaban hukumar ya kuma yi bayani kan tuhume-tuhumen da ake masa.

    Shugaban EFCC ya ce duk da kiran wayar, tsohon gwamnan bai amsa gayyatar ba.

    Yahaya Bello dai ya musanta gayyatar da aka yi masa inda ya ƙalubalanci EFCC ta gabatar da kwafin takardar gayyatar da ta aike masa.

    Cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran tsohon gwamnan ya fitar, Yahaya Bello ya zargi EFCC da yaɗa jita-jita.

    Shugaban EFCC ya ce "Idan har ban ga ƙarshen binciken da ake yi wa Yahaya Bello ba, zan ajiye aikina a matsayin shugaban EFCC.

    "Na gurfanar da tsoffin gwamnoni biyu da a yanzu aka ba su beli - Willie Obiano da Abdulfatah Ahmed. Da mun bi Bello tun Janairu amma muka jira umarnin kotu.

    "Idan har na iya gurfanar da Obiano da Abdulfatah Ahmed da Chief Olu Agunloye, me zai sa ba zan gurafanar da Yahaya Bello ba?

    Olukoyode ya kuma ce tsohon gwamnan ya kwashi dala dubu 720 daga asusun gwamnati kafin barin mulki domin biyan biyan kuɗin makarantar ɗansa.

    Tsohon gwamna Bello ya roƙi babbar kotun tarayya a Abuja da ta soke izinin kama shi da aka bai wa EFCC ranar 17 ga watan Afrilu.

    • Abin da masana ke faɗi kan masu hana EFCC ta kama Yahaya Bello
  11. Assalamu alaikum

    Barkan mu da warhaka. A yau Laraba muna fatan za ku kasance tare da shafinmu na kai tsaye domin samun labaran ƙasashen duniya musamman Najeriya da maƙwabtanta.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta - Fesbuk da X da Instagram inda za ku karanta ƙarin labarai da kallon bidiyo.

    Da fatan za ku kasance tare da mu tsawon yinin wannan rana domin sanin halin da duniya ke ciki.