Yarinyar da ta auri ɗan shekara 63 a Ghana ta kusa 16 – minista
Ministan harkokin masarautu da harkokin addini na Ghana ya bayyana cewa yarinyar da ta auri wani jagoran addinin gargajiya mai shekara 63 da aka ruwaito shekararta 12, a zahiri ministan ya ce shekararta 15.
Minista Stephen Asamoah Boateng ya bayyana haka a wata hira da gidan rediyon Citi FM cewa yarinyar za ta cika shekara 16 a watan Yuli.
Duk da saɓanin shekarun da aka samu, ministan ya jaddada cewa yarinya ce, kuma ya ce za a yi ƙoƙarin kare haƙƙinta tare da haɗin gwiwar wasu hukumomi.
Sabanin bayanin da ministan ya yi, basaraken al’ummar Nungua, inda aka gudanar da bikin, ya shaida wa Citi FM cewa yarinyar tana shekara 13 ne kacal.
Mafi ƙarancin shekarun aure a dokar Ghana shi ne shekara 18.
Bayyanar shekarun yarinyar na gaskiya ya janyo cece-ku-ce a tsakanin jama'a sakamakon yaɗa faifan bidiyon ɗaurin auren nasu a ranar Asabar a shafukan sada zumunta.
A ranar Litinin ne ‘yan sanda suka sanar da cewa sun gano yarinyar kuma za su tabbatar da tsaronta yayin da suke gudanar da bincike a kan auren da ya janyo cece-kuce.
A halin da ake ciki, ofishin jagoran addinin gargajiya ya kare bikin, yana mai bayyana shi a matsayin baiko tare da tabbatar da cewa yarinyar ba za ta fara sauke nauye-nauyen aure ba a wannan lokaci.
Dangane da lamarin, mataimakiyar babban mai shari’a Diana Asonaba Dapaah ta umurci ‘yan sanda da su gudanar da cikakken bincike inda ta bayyana cewa aure ko wane iri na ƙaramar yarinyar da ba ta kai shekara 18 ba ya saɓawa dokar ƙasar kuma akwai hukunci.
- Auren wuri haramun ne - Save the Children
- 'Babu wani aibu a auren wuri'