Shugaban Rwanda zai gana da shugaban DR Congo kan rikicin ƙasashen biyu
Shugaban ƙasar Rwanda Paul Kagame ya amince da ganawa da takwaransa na jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo domin ƙokarin kawo ƙarshen rikici tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda tashar Rediyo Okapi da Majalisar Dinkin Duniya ke daukar nauyi ta ruwaito
Sanarwar ta biyo bayan ganawar da Kagame da shugaban Angola Joao Lourenco suka yi a birnin Luanda, wanda ƙungiyar Tarayyar Afirka ta buƙaci sasantawa tsakanin Rwanda da DR Congo.
Fadar shugaban kasar Rwanda ta fada a shafin X cewa Kagame da Lourenco "sun amince da muhimman matakai don magance tushen rikice-rikice a gabashin DR Congo da kuma buƙatar kiyaye matakan Luanda da Nairobi don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin rikicin yankunan”.
A watan Fabrairu ne Lourenco ya gana da Tshisekedi domin tattauna halin da ake ciki a gabashin DR Congo yayin da Angola ke ƙara kaimi a fannin diflomasiyya don kawo ƙarshen faɗa tsakanin sojojin Kongo da kungiyar 'yan tawayen M23, wadda ake zargin Rwanda ce ke marawa baya.
A cewar ministan harkokin wajen Angola, shugaban DR Congo ya kuma amince da yin shawarwari da Kagame, amma babu tabbacin hakan daga Kinshasa.
A nasa ɓangaren, kakakin gwamnatin Rwanda a jiya ya yi Allah wadai da zargi "marasa mutunci" da ministan harkokin wajen DR Congo Christophe Lutundula ya yi na cewa Rwanda na amfani da kisan kiyashin da aka yi wa 'yan ƙabilar Tutsi a shekarar 1994 a matsayin wani "tsabar ciniki ta siyasa".
Ana zaman ɗar-ɗar tsakanin ƙasashen biyu dake makwabtaka da juna bisa zargin goyon bayan 'yan tawayen juna.
- Rwanda: An kashe 'yan tawayen Hutu 19
- Yadda aka ƙona motum 20 har lahira ciki har da marasa lafiya a Kongo