Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Nabeela Mukhtar Uba and Habiba Adamu

  1. Yau ce rana ta ƙarshe ta tattaunawa don warware rikicin siyasa a Senegal

    A yau ne aka kawo karshen taron kwanaki biyu na taron kasa da shugaban kasar Senegal Macky Sall ya kaddamar a daidai lokacin da shugabannin siyasar kasar ke kokarin warware rikicin siyasar da ba a taba ganin irinsa ba, sakamakon ɗage zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a wannan watan zuwa Disamba.

    Shafin yaɗa labarai na PressAfrik ya bayar da rahoton cewa, Sall ya shaida wa mahalarta taron a jiya cewa, a wannan makon ne majalisar za ta amince da yi wa jiga-jigan ƴan siyasa da ake tsare da su daga shekarar 2021 zuwa 2024 afuwa gaba daya, domin sassauta takun-saka dangane da ɗage zaɓen.

    Shugaban ya ce tattaunawar da mutum 17 daga cikin 19 da aka tabbatar sun kauracewa zaɓen na da nufin cimma matsaya kan ranar da za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da aka ɗage.

    Wa'adin shugaba Sall dai zai ƙare a ranar 2 ga watan Afrilu, amma ba zai yiwu a kammala tsarin zaɓen wanda zai gaje shi ba a lokacin.

    • Manyan tambayoyin da shugaban Senegal ya ki amsawa a jawabinsa
    • Ɗage zaɓen Senegal ya saɓa wa ƙundin tsarin mulkin ƙasar - kotu
  2. Mataimakin Ten Hag zai bar Manchester United

  3. Babban bankin Najeriya ya ƙara yawan kuɗin ruwa

    Gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Yemi Cardoso ya sanar da ƙarin kuɗin ruwa zuwa kashi 22.75 cikin ɗari daga kashi 18. 75 cikin ɗari a bara.

    Cardorso ya bayyana hakan ne bayan kammala taron manufofin kuɗaɗe na ƙasar na farko tun bayan zamansa shugaban CBN, da aka yi a Abuja a ranar Talata.

    Mista Cardoso ya ce an dauki wannan matakin ne da manufar dakile hauhawar farashi da kasar ke fama da shi.

  4. Yadda masu zanga-zanga suka kutsa cikin Majalisar dokokin Najeriya

  5. Ƙungiyar malaman Senegal sun yi watsi da yin zabe a watan Yuli

    Ƙungiyar malamai ta ƙasar Senegal mai ƙarfin faɗa a ji, ta shure tayin da shugaban ƙasar, Macky Sall ya yi na yin zaben ƙasar a watan Yulin wannan shekarar.

    Shugaban ya bayyana hakan ne kwana ɗaya bayan wani taron ƙasa don tattauna sabuwar ranar da za a yi babban zabe, wanda ƴansiyasa da shugabannin addini suka ƙauracewa.

    "Ba mu yarda da yin zaɓe ba a duk wata ranar da ta wuce watan Afrilu. Ba ma so mu halarci taron bogi. Dole shugaban ya sake sanya wata sabuwar rana kafin biyu ga watan Afrilu. Abin da muke so ya yi ke nan," sakataren ƙungiyar, Ismael Ndiaye, ya shaida wa BBC.

    Mafiya yawan ƴan ƙasar ta Senegal musulmi ne kuma sanarwa daga ƙungiyar malaman na da babban tasiri. Shugabannin sun soki shugaba Sall da jinkirta zabe.

    Lamarin da a cewarsu ya shafa wa ƙasar baƙin fenti kan saninta da aka yi da ƙasa mai zaman lafiya a mulkin dimokradiyya, a yankin da ake fama da juyin mulkin soji da rashin tsaro.

    • Manyan tambayoyin da shugaban Senegal ya ki amsawa a jawabinsa
    • Ɗage zaɓen Senegal ya saɓa wa ƙundin tsarin mulkin ƙasar - kotu
  6. Ƴankasuwar Nijar sun yi watsi da ƙayyade farashin shinkafa

    Ƴankasuwa a jamhuriyyar Nijar sun bijire wa dokar da ministan kasuwacin kasar ya sanya wa hannu da ke ƙayyade farashin shinkafa a fadin kasar.

    Ƴankasuwar sun ce gwamnatin ta ɗauki matakin ne ba tare da yin shawara da su ba.

    Dan haka suka ce yin biyayya ga wannan doka zai haifar musu da asara, ko ma ya janyo musu karyewar jari.

    Shugaban ƴankasuwar Alhaji Sani Shekarau ya ce idan suka yi amfani da farashin gwamnatin za su iya durƙushewa.

    Al'ummar ƙasar ne suka fara kokawa kan rashin biyayyar da ƴankasuwar suka yi ga dokar.

    Ma'aikatar kasuwancin ta ce ta ɗauki matakin ƙayyade farashin shinkafar ne bayan ta yi la'akari da hauhawar farashinta da kuma irin wahalar da mutane ke sha.

    Wasu mazauna Yamai babban birnin ƙasar sun ce babu irin shinkafar da aka ƙayyade mata farashin a kasuwanni.

    • Farashin shinkafa zai tashin da bai taɓa ba cikin shekara 12 - MDD
    • 'Raba mana gwangwanin shinkafa a matsayin tallafi raini ne'
  7. Ɗan Najeriya da ke cikin shirin '90 Day Fiancé ya ɓata a Amurka

    Wani ɗan Najeriyan da ya yi suna a wani shirin gidan talbijin da ake nunawa a Amurka na haɗa masoya "90 Day Fiancé" ya yi ɓatan dabo a Amurkar tun ranar juma'a, in ji matarsa.

    Ba a san inda Michael Ilesanmi ya ke ba tun bayan lokacin da ya bar gidan da yake zaune tare da matarsa ba tare da ya ɗauki komai ba, Angela Deem, ta bayyana hakan a wani bidiyon da ta watsa kai tsaye ta dandalin TikTok. Ta ce an sanar da ƴansanda.

    Ma'auratan sun haɗu ne a Facebook suka yi aure a shekarar 2020, amma da fari Ilesanmi bai samu nasarar samun bizar Amurka ba.

    Amma daga bisani ya samu ya kuma tare da matarsa Deem a jihar Georgia a watan Disambar bara.

    Masoyan shirin na "90 Day Fiancé" na raɗe-raɗin yadda aka yi ya ɓace, saboda yadda ake nuna dangantakar ma'auratan cike da cin zarafi na baki da kuma na jiki a cikin shirin da abubuwan da hakan ya haifar.

    Ana nuna shirin ne a tashar TLC, wanda ke bibiyar zamantakewar masu auren ƴan ƙasashen waje.

    A mafi yawancin lokuta suna yin aure ne kwana 90 bayan sun samu bizar Amurka ta K-1 na masu baiko.

  8. Gwamnan Gombe ya jinjina wa yarinyar da ta lashe gasar karatun Al-Ƙur'ani ta duniya

    Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana farin cikinsa game da nasarar da Hajara Ibrahim Dan'azumi - wata matashiya ƴar jihar ta samu ta lashe gasar karatun Al-Qur'ani ta duniya da aka yi a ƙasar Jordan.

    An zaɓi Hajara Ibrahim daga makarantar Islamiyya ta Abubakar Siddiq wadda ɗaliba ce ƴar aji biyu da ke karatun ilimin tsirrai daga jami'ar jihar Gombe ta wakilci Najeriya, inda kuma ta lashe gasar cikin mutane daga ƙasa 39 da suka halarci gasar karo na 18 da ma'aikatar kula da harkokin musulunci da ba da zakka da hubusi ta Jordan ke shiryawa duk shekara.

    Da yake tsokaci kan batun, Gwamna Inuwa Yahata ya miƙa saƙon taya murna ga Hajara da danginta da kuma malamanta inda ya yaba da ƙoƙarinta da jajircewarta wajen haddace Al-Qur'ani.

    Ya kuma bayyana cewa nasarar da ta samu zai zama ƙwarin gwiwa ga mutane da dama da ke Gombe da wasu jihohin.

    Gwamnan ya jaddada muhimmancin kula da kuma tallafawa matasa ta ɓangaren karatunsu musamman na addini abin da ya ce yana taka rawa sosai wajen gyara halayyarsu da kuma ba da gudummawa ga ci gaban al'umma.

    • 'Yan Najeriya sun yi zarra a gasar karatun Kur'ani a Saudiyya
    • Yadda DPO ya lashe gasar karatun Al-Kur’ani a Kano
    • Abu biyar game da Liliana Mohammed, Baturiyar da ta sauke Ƙur'ani a Kano
  9. Yajin aikin likitoci a Koriya ta Kudu ya janyo mutuwar dattijuwa

    Gwamnatin Koriya ta Kudu ta ƙaddamar da bincike kan mutuwar wata mata dattijuwa bayan da aka hana motar ɗaukan marasa lafiya shiga asibitoci da dama saboda yajin aikin da likitoci suke a ƙasar.

    Mara lafiyar ta mutu ne cikin motar bayan da zuciyarta ta buga.

    Kusan kashi 70 cikin 100 na ƙananan likitoci na yajin aiki tun makon da ya gabata inda suke adawa da shirin horas da ƙarin likitoci.

    Matakin ya janyo matsi a ɗakunan bayar da agajin gaggawa inda gwamnati ke zargin likitocin da jefa rayuwar jama'a cikin haɗari.

    Jami'an da ke da ƙwarewar ba da agajin gaggawa a birnin Daejon ranar Juma'a sun kira kusan asibitoci bakwai domin kai dattijuwar sai dai dukkan asibitocin sun ƙi amincewa a kai matar saboda rashin likitoci da kuma gadaje.

    Daga bisani an kwantar da ita a asibitin jami'ar gwamnati, mintuna 67 bayan da ta fara kira domin neman agaji sai dai an bayyana cewa rai ya yi halinsa da isar su asibitin.

    A ranar Talata ne jami'an gwamnati suka ce za su yi bincike a kan lamarin, rahoton kuma ya karaɗe kafafan yaɗa labaran Korya ta Kudu.

    Ana ganin wannan ne rashi na farko da aka alaƙanta da yajin aikin likitocin inda likitoci masu neman ƙwarewa damasu sanin makamar aiki ke zanga-zanga kan ƙudurin gwamnati na ƙara yawan likitoci saboda fargabar gogayya.

    Yajin aikin dai ya sa an ɗage aikin tiyata sannan lamarin ya sa dole tura marasa lafiya zuwa wasu asibitoci, kamar yadda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ruwaito.

    • ‘Ɗan uwana ya kashe kansa yayin da nake ƙoƙarin hana wasu kashe kansu’
    • Yadda kunya ke hana mata neman hutu a lokacin jinin al'ada
    • Yadda matasa a Koriya Ta Kudu ke ado da takunkumi duk da wucewar Korona
  10. Masu gidajen burodi sun fara yajin aiki a Najeriya

    Ƙungiyar masu gidajen burodi ta Najeriya (AMBCN) ta ce ta dakatar da duk wasu ayyukanta daga yau 27 ga watan Fabarairu.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar, wadda ta samu sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Mansur Umar, ƙungiyar ta ce ta ɗauki wannan matsaya ce bayan kammala wani taron gaggawa na musamman da ta kira domin matsa wa gwamnati lamba kan ta ɗauki matakin sauƙaƙa kasuwancin masu sarrafa fulawa a ƙasar.

    Sanarwar ta ce duk wasu ayyukan haɗawa ko sayar da burodi ya kawo ƙarshe ne a jiya Litinin, 26 ga wata, kuma yajin aikin zai ci gaba har nan da mako ɗaya.

    Wannan dai zai ƙara dagula lamurra a ƙasar, daidai lokacin da ƙungiyar ƙwadago ta ƙasar - NLC ta kira zanga-zanga ta gama-gari.

    Najeriya dai na fama da tashin farashin kayan masarufi, lamarin da ya kai ga masu kamfanoni ƙara farashin kayan da suke samarwa sanadiyyar hauhuwar farashin kayan da suke amfani da su.

    Fulawa na ɗaya daga cikin kayan masarufi da farashinsu ya yi tashin gwauron-zabi tun bayan da ƙasar ta shiga cikin halin tangal-tangal na tattalin arziƙi.

    • Farashin burodi zai ninka nan gaba kaɗan, in ji masu gidajen burodi na Abuja
    • Yadda ake tsananin ƙarancin burodi a Gaza
  11. Ƴan ƙwadago sun isa gidan gwamnatin Kano domin miƙa buƙatunsu

    • Zanga-zangar da 'yan ƙwadago suka yi a sassan Najeriya
  12. 'Mutane na iya mutuwa idan muka ci gaba da ɗaga wa gwamnati ƙafa'

    Shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Najeriya, Joe Ajaero ya ce sun fito zanga-zanga ne a yanzu ganin cewa idan suka jinkirta yinta, mutane da dama za su iya mutuwa saboda tsananin halin matsi da jama'a ke ciki sakamakon tsadar rayuwa.

    Ajaero ya bayyana haka ne a yau yayin da ƙungiyar ke zanga-zangar yini biyu a faɗin Najeriya domin bayyana rashin jin daɗinta game da yanayin da ƙasar ke ciki.

    A hirarsa da manema labarai a dandalin zanga-zangar a Abuja, ya ce shugabannin Najeriya sun tabbatar da yadda mutane suka shiga garari sakamakon matsin rayuwa sai dai a cewarsa, abin da gwamnati ke cewa a kullum shi ne a ba ta lokaci.

    "Shi ne muke cewa idan aka ci gaba da haƙuri, to kowa na iya mutuwa kafin lokacin da za a yi wani abu, ku yi wani abu yanzu, shi ne kawai banbanci." in ji shi.

    "Muna duba lokacin, muna son a yi wani abu cikin gaggawa kafin wata shekarar, dole mutane su rayu kafin su ji ci gajiyar aikin." kamar yadda ya ce.

    Ajaero ya ce yana da yaƙini cewa shugaba Tinubu zai yi wani abu game da halin da jama'a ke ciki.

    Shugaban na NLC ya ce babu wani ma'aikaci da zai rayu kan mafi ƙanƙantar albashi na naira dubu talatin inda ya ce fiye da ƴan Najeriya miliyan ɗari da hamsin ba su ƙetara layin fatara ba wato a cewarsa, ba sa iya samun abin kai wa baka a kullum.

  13. Hotunan yadda zanga-zangar tsadar rayuwa ke gudana a Legas

  14. Ƴan ƙwadago sun kutsa cikin majalisar dokokin Najeriya

    Ɗaruruwan masu zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Abuja, babban birnin Najeriya sun nufi majalisar dokokin ƙasar.

    Shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC, kwamared Joe Ajeoro ne yake jagorantar zanga-zangar.

    Wakilin BBC Hausa da ke inda ake zanga-zangar ya ruwaito cewa jami'an tsaro da suka haɗa da ƴan sanda da na Civil Defense na ƙoƙarin hana su shiga harabar majalisar.

    Sai dai a cewar wakilin BBC duk da turjiyar da jami'an tsaro suka nuna don hana ƴan ƙwadagon shiga harabar majalisar, hakan bai hana su ture shingen da aka saka ba inda suka shiga da ƙarfi sakamakon yawan da suke da shi.

    Masu zanga-zangar dai sun toshe manyan hanyoyin da suka haɗa tsakiyar birnin tarayya Abuja.

    Sun fara taruwa ne a hedikwatar NLC a Abuja inda a yanzu suka nufi majalisar dokokin ƙasar.

  15. Hotunan ƴan ƙwadago da ke zanga-zanga a Abuja

  16. Kwastam ta tabbatar da mutuwar mutane a turmutsitsin raba shinkafa, Daga Mansur Abubakar, BBC News

    Hukumar kwastam a Najeriya ta tabbatar cewa turmutsutsin da aka yi a baya-bayan nan a cibiyar sayar da shinkafa a farashi mai rahusa ya janyo mutuwar mutane tare da jikkatar wasu.

    Hukumar tana sayar da shinkafa ne kan farashi mai rahusa ga ƴan Najeriya daidai lokacin da farashin kayan masarufi ke ƙaruwa a sassan ƙasar.

    A makon da ya gabata ne, kwastam ta ce za ta rarraba kayan abincin da ta ƙwace da ke ajiye a rumbunanta domin magance matsalar tsadar abinci a faɗin ƙasar.

    Ana sayar da buhu mai mauyin kilogram 25 na shinkafar da aka ƙwace sakamakon haramcin shigo da ita daga wasu ƙasashen kan naira dubu goma abin da ya janyo dandazon mutane a wurin kasancewar ana sayar da irin buhun shinkafar kan naira dubu arba'in.

    Sai dai lamarin ya sauya bayan da jami'an kwastam suka faɗa wa taron jama'ar su sake komawa washegari saboda shinkafar ta ƙare.

    Kwastam ta ce mutanen sun kutsa kai domin neman buhun shinkafa cikin kwantenonin da ba komai cikin su.

    Ta ce lamarin ya janyo turmutsistin jama'a har ta kai ga mutuwar mutane da jikkatar wasu.

    • Hukumar Kwastam: 'Al'umma ke taimaka wa ɓata gari wurin shigo da kwayoyi'
    • Ƙarin hauhawar farashin da aka daɗe ba a gani ba na gigita ƴan Najeriya
  17. Abin da ministan kuɗin Najeriya ya ce kan zanga-zangar NLC

    Ministan kuɗi a Najeriya, Wale Edun ya ce gwamnati ta ɗauki wasu manyan matakan sauye-sauye a tattalin arzikin ƙasar da ya kamata a ce tuntuni an yi su waɗanda ya ce yanzu da aka yi ana jin raɗaɗin hakan.

    Ministan yana magana ne game da zanga-zangar yini biyu da ƙungiyar ƙwadago ta kira yau da kuma gobe Laraba domin nuna takaici kan yadda al'umma ke fama da tsadar rayuwa a Najeriya.

    Yanzu haka tashin farashin kayan masarufi a ƙasar ya kai kimanin kashi 30 cikin 100 yayin da darajar takardar naira ke ci gaba da zubewa.

    Matsalar ƙarancin lantarki na ƙara dagula al'amura.

    Bankin ci gaban ƙasashen nahiyar Afirka ya yi gargaɗin cewa za a iya fuskantar tashin hankali a ƙasar saboda yunwa.

    Ministan ya faɗa wa BBC cewa "Shugaba Bola Tinubu ya duƙufa wajen cika alƙawurran da ya ɗaukar wa ƴan Najeriya na cewa ba za a bar talakawa da masu rauni a baya ba."

    Ya ce "saƙona shi ne na sake jaddada abin da shugaban ƙasa ya ce, cewa sauye-sauyen nan sun zama dole kuma yana jin raɗaɗin sannan yana ƙoƙari na ganin ya rage shi tare da taimaka wa waɗanda suka fi fuskantar matsi kuma yana ɗora ƙasar kan turbar farfaɗo da tattalin arziki kuma ya buƙaci mutane su ƙara haƙuri a wannan lokacin sannan yana yin duk mai yiwuwa na rage raɗaɗi da taƙaita lokacin da hakan zai ɗauka."

    Ministan ya bayyana cewa abin da gwamnati ke son yi shi ne samar da isasshen abinci da samun isassun kayan da ake nomawa a ƙasar.

    Ya bayyana cewa tashin dalar ya faru ne sakamakon hauhawa kuma a cewarsa, gwamnati ta yi ɗamara na rage hauhawar farashin kayayyaki.

    Ya ƙara da cewa idan har masu zanga-zanga suka tunkare shi, zai nemi su bai wa sauye-sauyen lokaci domin su yi aiki.

    Najeriya na tsaka da halin matsin rayuwa inda farashi ke tashin gwauron zabi da kashi 30 cikin 100 a shekara yayin da darajar naira ke ƙara raguwa.

    • Wace dabara ta rage wa Tinubu game da tsadar rayuwa a Najeriya?
    • Yadda farashin kayan masarufi ya tashi a lokacin mulkin Tinubu
    • Ƙarin hauhawar farashin da aka daɗe ba a gani ba na gigita ƴan Najeriya
  18. Yadda ƴan ƙwadago suke hallara domin zanga-zangar tsadar rayuwa a Kano

  19. Ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya na zanga-zanga kan matsin rayuwa

    A yau ne ƙungiyoyin kwadago a Najeriya ke zanga-zanga saboda tsadar rayuwar da al'umma ke fuskanta a ƙasar.

    Ƙungiyar kwadagon ta ce za ta yi zanga-zangar ne na yini biyu - Talata da Laraba.

    Hauhawar farashi a ƙasar wadda tattalin arzikinta shi ne mafi girma a Afirka ya kai kusan kashi 30 cikin 100 yayin da darajar naira ke ci gaba da karyewa.

    Matsalar rashin wuta na daga cikin abubuwan da ke ƙara ta'azzara halin matsin da ake ciki a ƙasar.

    Bankin raya ƙasashen Afirka AfDB ya yi gargaɗin cewa halin da ake ciki na iya janyo bore a ƙasar duk da cewa tuni wasu jihohin ƙasar suka yi makamanciyar zanga-zangar ta tsadar rayuwa.

    Gwamnati ta ce za ta rage kuɗin da take kashewa wajen tafiyar da harkokinta sannan ta yi alƙawarin ɗaukan matakai domin taimakawa al'umma da kuma masu ƙananan sana'oi.

    Babu bayanai kan yawan ma'aikatan da za su shiga zanga-zangar saboda mutane da dama na zargin ƙungiyoyin da rashawa.

    • Zanga-zangar da 'yan ƙwadago suka yi a sassan Najeriya
    • Kalaman 'yan Najeriya bayan sake ƙara kuɗin man fetur
  20. Barkan mu da warhaka

    Daga nan BBC Hausa muke yi muku barka da warhaka.

    Muna fatan za ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.