Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida, Haruna Kakangi, Ahmad Tijjani Bawage and Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Jagoran 'yan adawa a Tunisiya ya fara yajin cin abinci

    Shugaban jam'iyyar Ennahda da ke adawa a Tunisiya, Rached Ghannouchi, ya shiga yajin cin abincin da wasu fursunonin siyasa ke yi domin cika shekara guda da fara tsare su.

    Mista Ghannouchi - wanda shugaban Tunisiya Kaïs Saïed ya zarge shi da yunƙurin juyin mulki - an yanke masa hukuncin ɗaurin shekara uku a farkon wannan watan bayan da aka same shi da laifin karɓar kuɗaɗe daga waje.

    Shugaba Saïed ya rufe hedikwatar jam'iyyar Ennahda, ya daure manyan 'yan adawar siyasa da kuma 'yan jarida masu sukar gwamnati da kuma rage 'yancin cin gashin kan kotunan ƙasar.

    Yana mai cewa matakan sun zama dole don hana hargitsi da kawar da cin hanci da rashawa.

  2. Gobara ta ƙona rumbun adana magunguna a Gombe

    Wata gobara ta ƙona rumbun adana magunguna a jihar Gombe.

    Gobarar wadda ta tashi da asubahin yau Litinin, ta lalata miliyoyin allurai tare da janyo rasa kayayyaki na biliyoyin naira.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Ibrahim Uba Misilli ya fitar, ta ce ta ce rumbun ya kasance yana ɗauke da alluran riga-kafin cutar shan-inna sama da miliyan biyu da kuma sauran magunguna.

    A ziyara da ya kai wurin da abin ya faru, gwamna Inuwa Yahaya ya nuna damuwarsa, inda ya ce hakan babban koma-baya ne ga jihar ta Gombe, musamman ma a daidai lokaci da take shirin kaddamar da fara riga-kafin polio a watan Maris.

    Gwamnan ya yi kira ga ƙungiyoyin ba da agaji da masu ruwa da tsaki a ɓangaren lafiya da su kawo wa jihar ɗauki, inda ya nanata rawar da rumbun ke taka wa wajen tallafawa ɓangaren lafiya ba ga jihar kaɗai ba har ma faɗin arewa maso gabas.

    Sauran kayayyaki da gobarar ta ƙona sun haɗa da na'urorin firji, da silinda, na'urorin sanyaya ɗaki da kuma babura.

    Rumbun mai tsawon shekara 60, wanda a baya aka yi amfani da shi don ajiye allurar COVID-19 a cikinsa a 2020, ya taka muhimmiyar rawa a matsayin wurin adana allurar riga-kafin kafin rarraba su zuwa zuwa wasu jihohin arewa maso gabas.

    Ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano asalin abin da ya haddasa gobarar.

  3. Barazanar Al-Shabab na kawo cikas ga aikin gina hanyoyin gabashin Afirka

    Barazanar hare-haren kungiyar Al-Shabab na kawo cikas ga yunkurin da wani dan kwangilar kasar China ya yi a farkon watan Febarairu na dawo da aiki a hanyar da ta hada Kenya da ke cikin hanyar da ta ratsa Sudan ta Kudu zuwa Habasha kamar yadda Jaridar Daily Nation ta Kenya ta ruwaito.

    Jaridar ta ce a jiya ne dan kwangilar ya yi watsi da wurin da ake aikin hanyar Lamu-Ijara zuwa Garrisa, inda aka kashe akalla mutum 16 tare da raunata 40 a hare-haren kungiyar al-Shabab tun daga shekarar 2021.

    Jaridar ta kuma ce an lalata kayayyakin gine-gine na dala miliyan 1.37 a akalla hare-hare hudu tsakanin shekarar 2022 zuwa 2023, inda aka kashe injiniyoyi da ma'aikata, lamarin da ya sa aka dakatar da ayyukan na wucin gadi.

    An bayar da rahoton hari na karshe a watan Disambar 2023.

    Jaridar ta ruwaito wani injiniyan gwamnatin Kenya na cewa an karfafa matakan tsaro a cikin shirin gina sassa na tsawon kilomita biyar har sai an kammala ayyukan, wanda a halin yanzu watanni 10 ke bayan jadawalin.

  4. Zaftarewar ƙasa ta kashe mutane 25 a Afganistan

    Aƙalla mutane 25 ne suka mutu bayan zaftarewar ƙasa sakamakon dusar ƙanƙara da ta mamaye wani ƙauye a Afganistan.

    Ya zuwa yanzu dai an san mutane takwas ne suka jikkata a lamarin, kuma ana fargabar adadin waɗanda suka mutu zai ƙaru.Jami’ai sun ce yanayin ya kawo cikas ga aikin ceto, inda jirage masu saukar ungulu suka kasa sauka a yankin sannan dusar kankara ta toshe hanyoyin.

    An tilastawa waɗanda suka yi nasarar isa ƙauyen da ke gabashin lardin Nuristan yin amfani da shebur da gatari wajen tono ɓaraguzan gine-ginen da suka rushe.

    Jami'in yaɗa labarai da al'adu na lardin, Jamiullah Hashimi ya shaidawa kanfanin dilancin labaren AFP cewa dusar ƙanƙara na ci gaba da fadowa duk da cewa mutane na ƙoƙarin kaiwa ga waɗanda suka tsira da rayukansu a ƙauyen Nakre.

    Ya kara da cewa "babu kayan aiki na zamani, da za su taimaka wurin aikin ceto".

  5. An samu ɗan ƙasar Senegal da laifin kashe ƴan ci-rani

    An samu wani matuƙin jirgin ruwa ɗan ƙasar Senegal da laifin kisan wasu baƙin haure huɗu da suka nutse a ruwa a lokacin da suka shiga matsala.

    Ibrahima Bah, wanda shi ma baƙon haure ne, ya yi tayin tukin jirgin a watan Disamba na shekara ta 2022 don shi ma ya sami damar yin tafiya a kyauta.

    Ya yi iƙirarin cewa ‘yan fasa-kwauri ne suka tilasta masa yin tafiya tare da aƙalla wasu bakin haure 43.

    Wani alƙali a kotun Canterbury Crown na Burtaniya ya kuma sami Bah da laifin taimakawa wajen karya dokar shige da fice.

  6. Wa ya fi yawan tafiye-tafiye zuwa ƙasashen waje tsakanin Tinubu da Buhari?

  7. Ba na da masaniya kan sakin Murja Kunya - Abba Kabir

    Gwamnatin jihar Kano ta ce ba ta da masaniya kan sakin fitacciyar 'yar TikTok Murja Ibrahim Kunya.

    Mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature, ya shaida wa BBC cewa gwamna Abba Kabir ba shi da masaniya kan kama ita Murja.

    ''Ba mu da masaniya kan wa ya saki Murja, bangaren shari’a ne zai iya ba da bayani kan haka,’’ in ji Sanusi Bature.

    Ya ce gwamna Abba Kabir Yusuf ba ya shiga harkar da ta shafi bangaren shari’a.

    Kakakin gwamnan ya ce batun bai kai wani al’amari ba da zai kai ga gwamnati ta saka baki.

    ''Mai girma gwamna ba ya nan ya tafi hutu, kuma bai kamata a alakanta shi da wannan karamin al’amari ba,'' in ji Sanusi Bature.

    Ya ce girman kujerar gwamna ta fi a alakanta ta da batun saboda mutum sama da miliyan 20 yake mulka a jihar Kano.

  8. Kalli yadda aka yi zanga-zangar tsadar rayuwa a Ibadan

  9. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da kisan mutum 12 a Kajuru

    'Yan bindiga sun kashe aƙalla mutane 12 tare da kona gidaje kusan 20 a wasu kauyuka na jihar kaduna ta Najeriya.

    Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi a ƙauyen Gindin Dutse Makeli da ke karamar hukumar Kajuru.

    Harin ya zo ne kwanaki kaɗan bayan ƴan bindigar sun kashe mutane shida tare da sace wasu 60 a kauyukan Kwassam da Sabon Layi karamar hukumar Kauru.

    A tattaunawar sa da BBC, kwamishinan riƙo na tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan, ya ce yanzu haka jami'an tsaro na yin bakin ƙoƙarin su wajen ganin sun shawo kan lamarin.

    Aruwan ya ce lamarin bai yi wa gwamnatin jihar daɗi ba kuma tuni suka aika da ta'aziyyar su ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.

    Sai dai kwamishinan ya bayyana cewa babu wani bayani kan ko maharan na ƙauyen Gindin Dutse sun yi garkuwa da wasu mutanen.

  10. 'Yan takarar Senegal sun yi kira da a kaɗa kuri'a cikin makonni shida

    'Yan takara 15 daga cikin 20 da aka amince su tsaya takara a zaɓen shugaban ƙasar Senegal da aka ɗaga sun buƙaci da a gudanar da sabuwar kuri'ar nan da ranar 2 ga watan Afrilu - ranar da shugaba Macky Sall na yanzu zai kawo karshen wa'adinsa.

    'Yan takara 15 kuma sun dage da cewa bai kamata a sauya jerin sunayen ba.

    Takardar ta samu sa hannun wasu daga cikin manyan ‘yan takarar da suka hada da Bassirou Diomaye Faye da ake tsare da shi bisa zargin tayar da hargitsi da kuma tsohon magajin garin Dakar Khalifa Sall, wanda ba shi da alaƙa da shugaban ƙasar.

    Shugaba Sall ya so ɗage zaɓen na wasu watanni domin a iya warware takaddamar cancantar wasu 'yan takara.

    Sai dai babbar kotun ƙasar ta ce ɗagewar ya saɓawa kundin tsarin mulkin kasar kuma Mista Sall ya ce a yanzu za a gudanar da zaben "da wuri-wuri".

  11. Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 da ƙona gidaje a jihar Neja

    Rahotanni daga ƙaramar hukumar mulkin Shiroro a jihar Neja na cewa wasu da ake zargin mayaƙan kungiyar Boko Haram ne sun kashe sama da mutum goma sha biyu tare da ƙona kimanin gidaje talatin a wasu jerin hare-hare da suka kai.

    Mazauna yankunan sun ce hare-haren sun faru ne a tsawon makon da ya gabata, a garuruwan Alawa da Bangajiya da sauran su, inda baya ga kashe mutane da dama da maharan suka yi sun kuma yi awon gaba da dukiya mai ɗimbin yawa.

    Wani Mazaunin garin ya shaida wa BBC cewar sama da makonni biyu ke nan suke fama da tashe tashen hankula na hare-haren ƴan bindiga waɗanda suka hana su sukuni.

    A cewar sa, a makon da ya gabata ne ƴan bindigar suka dasa bam a hanya wanda ya tashi da wasu da ke kan hanyar komawa ƙauyukansu daga kasuwa kuma nan take mutane aƙalla takwas suka rasa rayukansu.

    Da aka je kwashe gawawwakin waɗanda aka kashe kuma aka sake kai wani harin da ya yi sanadiyar asarar rayuka sannan suka hana daukar gawawwakin wanda har ya zuwa yanzu babu labarin kwashe gawawwakin.

    Shugaban ƙaramar Hukumar Shiroro Hon. Akiku Kuta ya tabbatar da harin

    Wadannan sabbin hare-haren dai sun sa mutane da dama yin hijira zuwa wasu makwabtan garuruwa

    • 'Rashin haɗin kan gwamnatoci dama ce ga 'yan bindiga'
    • Ƴan bindiga sun kai harin ramuwa a Zamfara
  12. Kamfanin AEDC ya yi barazanar yanke wa fadar shugaban Najeriya wutar lantarki

    Kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja AEDC ya yi barazanar katse wutar lantarki a fadar shugaban Najeriya da na wasu ma’aikatun gwamnati 86 a kan bashin kuɗin wuta sama da naira biliyan 47 da yake bin su.

    Wasu daga cikin ma'aikatun da barazanar ta shafa sun haɗa da ma'aikatar kuɗi da ta yaɗa labarai da ta kasafin kuɗi da ta ayyuka da gidaje, da gwamnan CBN da ofishin Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) da sauran su.

    A cikin sanarwar da kamfanin ya fitar a ranar Litinin, AEDC ɗin ya bai wa ma'aikatu da ofisoshin na gwamnati kwana 10 domin biyan basukan ko kuma a yanke musu lantarki, wato daga 28 ga watan Fabarairun 2024.

    Bangaren samar da wutar lantarki a Najeriya dai ya shafe shekaru yana fama da matsalar bashi.

    A makon da ya gabata ne Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce umarci kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) da su tashi tsaye idan ba haka ba duk wanda aka samu da laifi, za a soke lasisin sa.

    • Yadda cire tallafin wutar lantarki a Najeriya zai shafe ku
    • Mene ne babban layin wutar lantarki na Najeriya kuma yaya yake aiki?
  13. Putin ne ya kashe mijina - Matar Navalny

    Yulia Navalnaya, uwargidar jagoran ƴan adawa na Rasha Alexi Navalny ta ce shugaban Rasha, Vladimir Putin ne ya kashe mijin nata.

    Ta faɗi hakan ne a wani jawabi da ta yi ta bidiyo.

    Ta ce, "Ya kamata a ce Navalny ne a nan wurin da na zauna. Amma Vladimir Putin ya kashe shi."

    "Putin bai kashe Navalny a matsayin mutum kawai ba amma yana so ya kashe begenmu da 'yancinmu, da kuma makomarmu"

    "Mun san ainihin dalilin da ya sa Putin ya kashe Navalny kwanaki uku da suka wuce. Za mu gaya muku nan ba da jimawa ba." in ji ta

    "Amma, abu mafi mahimmanci da za mu iya yi wa Navalny da kanmu shi ne ci gaba da fafutika."

    "Zan ci gaba da aikin da Alexei Navalny ya fara, zan ci gaba da gwagwarmaya domin kasarmu. Kuma ina kira ga dukkan ku da ku tsaya tare da ni."

    "Ina kuma rokon ku da ku nuna fushi da ƙiyayya ga waɗanda suka yi ƙoƙari su kashe makomarmu."

    Putin dai har yanzu bai ce komai ba game da mutuwar Navalny.

  14. Martanin shugabannin ƙasashen yamma kan mutuwar Navalny

    Bayan mutuwar Alexei Navalny, shugabannin duniya da dama sun yaba masa a matsayin fitaccen dan siyasar Rasha, sannan kuma sun dora laifin mutuwarsa kan fadar Kremlin.

    Ga wasu taƙaitaccen bayani kan abin da wasu daga cikin shugabannin suka ce:

    • Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ce bisa ga dukkan alamu Navalny ya biya jajircewarsa da rayuwarsa.
    • Navalny ya kasance babban mai ba da shawara ga dimokiradiyyar Rasha, a cewar Firayim Ministan Burtaniya Rishi Sunak.
    • Shugaban Amurka Joe Biden ya ce mutuwarsa a gidan yari ya fi shaida irin ta'asar Vladimir Putin.
    • Moscow ta yi watsi da zargin da ake mata na kashe Navalny
  15. Rwanda ta caccaki sukar Amurka kan tashe-tashen hankula a DR Congo

    Ƙasar Rwanda ta caccaki Amurka kan sukar da ta yi game da ƙaruwar tashe-tashen hankula a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, yayin da ta nuna matukar damuwa kan abin da ta kira watsi da shirin samar da zaman lafiya a yankin.

    A cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar Rwanda ta fitar, Rwanda ta kuma ce kasashen duniya ba su nuna halin ko-in-kula da "aikin da sojin DR Congo ke yi ba", ta kara da cewa gagarumin aikin da kasar ta yi a gabashin yankin Kivu da ke gabashin kasar ya saba wa shawarwarin da wasu hanyoyin yankin suka dauka.

    Dakarun kungiyar raya kasashen kudancin Afirka (SADC) na taimakawa sojojin DRC wajen tunkarar kungiyoyin da ke dauke da makamai ciki har da kungiyar M23.

    A makon da ya gabata ne wasu sojojin Afirka ta Kudu biyu da ke cikin dakarun SADC suka mutu, yayin da uku suka jikkata bayan da wani bam ya fado a sansaninsu.

    A karshen mako, Amurka ta yi Allah wadai da zargin goyon bayan da Rwanda ke yi wa dakarun M23 na Congo tare da yin kira ga kasar da ke gabashin Afirka da ta gaggauta janye dukkan dakarunta daga DR Congo.

    Rwanda ta musanta goyon bayan M23.

    Sanarwar da kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka ya fitar ta bukaci Rwanda da ta cire na'urorinta na makami mai linzami da ke DR Congo, lamarin da ta ce yana barazana ga rayukan fararen hula, da dakarun wanzar da zaman lafiya da jiragen kasuwanci.

    Rwanda ta ce furucin na Amurka ya gurbata gaskiyar lamarin, inda ta ƙara da cewa matakin da DR Congo ke yi na barazana ga tsaronta, kuma tana da hakkin daukar matakan kare kanta daga wannan barazana.

    Ta ce za ta nemi ƙarin haske daga Amurka saboda sanarwar ta saɓawa salon tsarin karfafa gwiwa da daraktan tattara bayanan sirri na Amurka ya kaddamar a bara.

  16. 'Babu sakamako' a binciken mutuwar Navalny - Kremlin

    Kakakin Kremlin, Dmitry Peskov ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutuwar Navalny amma har zuwa safiyar Litinin babu wani sakamako "har yanzu".

    Binciken, ya ƙara da cewa, "ana gudanar da binciken bisa ga dokar Rasha".

    Kakakin ya kuma ɗauki wani lokaci wajen kare shugaban kasar Rasha Vladimir Putin bisa zargin da shugabannin kasashen yammacin duniya ke yi masa na cewa shi ne ke da alhakin mutuwar Navalny.

    Peskov ya ce "Mun yi la'akari da cewa ba za mu yarda da irin waɗannan maganganun banƙyama ba."

    “Haƙiƙa wadannan kalamai ba za su iya kawo barna ga shugaban kasarmu ba." in ji Peskov

  17. Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta haramta safarar fatar jaki

    Ƙungiyoyin ba da agaji ga dabbobi sun yi maraba da dokar haramta safarar fatar jaki da aka kafa a faɗin Afirka.

    Wannan dokar dai ya haramta yanka jakai a ƙasashe 55 na Afrika.

    Shugabannin kasashen Afirka sun amince da haramcin ne a karshen taron kungiyar Tarayyar Afirka da aka kammala a kasar Habasha ranar Lahadi.

    Dr Onyango ya shaida wa BBC cewa haramcin zai kare jakai da kuma rayuwar miliyoyin da suka dogara da su.

    Buƙatar fatar jakan dai na da nasaba da shaharar wani maganin gargajiya da ake yi da fatar jaki me suna Ejiao a ƙasar China.

    Wasu sun yi imanin Ejiao yana da fa'idodin hana tsufa da kuma lafiyar jiki, kodayake wannan ba shi da tabbas.

    Wata ƙungiyar agaji mai suna 'The donkey sactuary ta kira wannan sana’ar na saye da sayaa da fatar jaki a matsayin “mummuna da rashin dorewa” inda ta ce sana'ar ta yi sanadin raguwar jakai a faɗin duniya musamman a kasashen Afirka da Kudancin Amurka.

    Kimanin kashi biyu bisa uku na adadin jakai miliyan 53 na duniya ana kiyasin suna Afirka ne.

    Ana kallon haramcin a matsayin wani muhimmin mataki na kiyaye wadannan dabbobi da kuma tallafawa al'ummomin karkara da suka dogara da su don jigilar kayayyaki da kuma ayyukansu na yau da kullum.

    • China ta rage harajin shigar da fatar jaki kasar
    • Kun san inda ake amfani da fatar jaki wajen maganin tsufa?
  18. Ana azumi kan tsadar rayuwa a jihar Borno

    Wasu 'yan Najeriya da dama a jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar sun fara azumi bayan da gwamnan jihar, Babagana Zulum ya yi kira da a roƙi "agaji daga Allah" kan matsalolin tattalin arziki da na tsaro da kuma kan tsadar rayuwa da ƙasar ke fuskanta.

    A ranar Juma’ar da ta gabata ne Zulum ya buƙaci al’ummar jihar su gudanar da azumin kwana guda a faɗin jihar a ranar litinin sakamakon tsadar kayan abinci a kasar.

    Bello Zabarmari, wani mazaunin jihar Borno, ya shaida wa BBC cewa shi da wasu da dama na azumi da addu'ar Allah ya warware musu matsalolinsu.

    “Mun tashi da azumi a yau kuma da fatan Allah zai amsa mana addu’o’inmu nan ba da jimawa ba, gwamnan ya yi abin da ya dace da kiran mutane da su yi azumi,” inji shi.

    Umar Shehu, wani mazaunin da ke aiki da hukumar kashe gobara ta jihar, ya ce shi da abokan aikinsa ma suna azumin kamar yadda gwamnan ya umarce su.

    ‘Yan Najeriya dai na cikin wani yanayi na tabarbarewar tattalin arzikin kasar mafi tsanani a tarihi inda farashin kayan abinci da kayan masarufi suka yi tashin gwauron zabi a ‘yan watannin nan.

    • Abubuwan da JNI ta faɗa kan tsadar rayuwa a Najeriya
    • Dalili hudu na yawan karyewar darajar naira
  19. Najeriya: Ana zanga-zangar tsadar rayuwa a Ibadan

    Dubban mutane sun hau kan titunan birnin Ibadan na jihar Oyo da ke kudu maso yammacin Najeriya domin nuna fushinsu kan tsadar rayuwa a Najeriya.

    Zanga-zangar ta fara ne daga yankin Mokola ta birnin, inda masu yin tattakin suka yi mahaɗa.

    Hakan na zuwa ne bayan gudanar da irin wannan zanga-zanga a jihohin Kano da Neja, inda mutane da dama suka fito domin kokawa kan matsalar tashin farashin kayan masarufi.

    Al'umma a Najeriya na fama da matsalar tashin kayan masarufi ne tun bayan da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ayyana cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayun 2023, jim kaɗan bayan ratsar da shi a matsayin shugaban ƙasa.

    Tun daga wancan lokacin ne farashin wasu kayan masarufi da abinci da sufuri suka nunka, lamarin da ya ƙara jefa al'ummar ƙasar cikin mawuyacin hali.

    Tun farko rundunar ƴansandan Najeriya a jihar Oyo ta gargaɗi masu zanga-zangar da su kauce wa duk wani abu da zai tayar da hankalin al'umma kuma ta bayyana cewa za ta tsaurara tsaro domin ganin lamarin bai rikiɗe zuwa tarzoma ba.

    Gwamnatin Najeriya dai ta bayyana cewa tana yin duk abin da ya kamata wajen sauƙaƙa wa al'umma halin matsin na rayuwa, inda ta ayyana wani shiri na tallafin kayan abinci da na masarufi ga al'umma.

  20. 'Neman Tinubu ya yi murabus karkatar da hankalin jama'a ne'

    Ministan yaɗa labarai da wayar da kai a Najeriya, Mohammed Idris ya yi watsi da kiraye-kirayen da ake na shugaba Bola Tinubu ya yi murabus inda ya ce yunƙuri ne na karkatar da hankalin mutane.

    A makon da ya gabata ne wasu gwamnoni daga jam'iyyar PDP, babbar jam'iyyar adawa a Najeriya suka buƙaci shugaba Tinubu ya ajiye muƙaminsa idan ba zai iya warware ƙalubalen tattalin arzikin da ƙasar ke fama da shi ba.

    A ranar Lahadi ne, Idris ya ce shugaba Tinubu ba zai ajiye aiki ba kuma yana da ƙwarewar magance taɓarɓarewar tattalin arziki.

    Cikin wata sanarwa, ministan ya ce matsalolin tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta ba su fi ƙarfin shugaba Tinubu ba kuma ba zai ajiye muƙaminsa ba.

    "Zai ci gaba da dagewa wajen yaƙar matsalolin har a samu galaba a kan su, shimfiɗa tubalin sabuwar Najeriyar da ke tasowa."

    Najeriya dai na fama da taɓarɓarewar tattalin arziki mafi muni cikin shekaru, inda darajar kuɗin ƙasar ke ƙara faɗuwa kuma jama'a da dama na fama wajen samun abin kai wa bakin salati.

    • Yadda farashin kayan masarufi ya tashi a lokacin mulkin Tinubu
    • Ko shigar da abinci Najeriya zai samar da mafita ga tsadar rayuwa?