Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yaba tare da karfafa wa kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles gwiwa bayan wasan da suka buga da Ivory Coast - mai masaukin baki wadda ta lashe gasar ta cin kofin Afirka ta 2023 da aka kammala ranar Lahadi.
Super Eagles sun yi rashin nasara a hannun Ivory Coast da ci biyu da daya, abin da ya kawo musu cikas a kokarin neman lashe kofin karo na hudu.
Duk da rashin nasarar, Shugaba Tinubu ya yaba da jajircewar da Super Eagles suka nuna.
Cikin wata sanarwa da mai bashi shawara kan yada labarai, Ajuri Ngelale, Shugaba Tinubu ya yaba wa kungiyar saboda kokarin da suka yi a gasar.
Shugaba Tinubu ya kuma bukaci yan kasa da kada su duba rashin nasarar da kungiyar ta yi, a maimakon haka su yi murna da nasarorin da Super Eagles ta yi.
A cewarsa, duk da rashin daga kofin a wannan karon, yana da yakinin Super Eagles ta samu babbar nasara a Afirka da duniya da irin kwallon da suka buga a filin wasa.
Ya kara da cewa bai kamata rashin nasarar ta sagar da gwiwoyin jama'a ba, hakan ya zama wani sanadin hada kan al'umma.
-
Nasarar Super Eagles da Ƙaddamar da sabbin jiregen yaƙi da wa'adin ƙungiyar kwadago
-
Yadda ƙwallo ke haɗa kan ƴan Najeriya, su manta da damuwarsu