Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida and Usman Minjibir

  1. EFCC ta kama wani fasto kan zargin aikata zamba

    Jami'an Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC sun kama shugaban wata coci a jihar Ebonyi, bisa zargin yi wa mabiya cocinsa da 'yan Najeriya zamba na tallafin kudin bogi daga wata gidauniya, wanda kudin ya kai naira biliyan 1,319,040,274.

    Wata sanarwa da hukumar ta EFCC ta fitar a yau Litinin ta ce an kama faston kan zargin damfarar wadanda tsautsayi ya fada mawa da suka hada da kungiyoyi masu zaman kansu na Najeriya da daidaikun mutane, ta hanyar tallata wani aiki da ake neman tallafi na kungiyarsa.

    Haka kuma EFCC din ta yi zargin cewar ya nemi wadanda lamarin ya shafa da su yi rajista tare da biyan kudin yin rajista, inda ya karbi naira milyan 1,800,000 daga hannun kowannen su, inda ya tara kudin da suka kai sama da naira biliyan daya.

  2. 'Yara 12 na mutuwa a kullum a sansanin ƴan gudun hijira na Sudan'

    Ƙungiyar ba da agajin lafiya ta medecins sans frontieres (MSF), ta yi gargadi game da wani mummunan yanayi na jin ƙai a sansanin ƴan gudun hijira da ke jihar Darfur ta arewa da ke Sudan.

    MSF ta ce ta ƙure duk wasu matakan gaggawa na rashin abinci mai gina jiki tare da yin kira da a ƙara kai agajin gaggawa na ƙasa da ƙasa.

    An ce aƙalla yaro ɗaya ne ke mutuwa duk bayan sa’o’i biyu a sansanin Zamzam da ke kusa da birnin Fasher.

    Yaƙin da ake gwabzawa tsakanin rundunar sojojin Sudan da kuma dakarun RSF ya raba kimanin mutane miliyan takwas da muhallansu tun daga watan Afrilun bara.

    Kimanin mutane miliyan biyar a faɗin ƙasar Sudan yanzu haka suna fuskantar matsalar yunwa, kamar yadda hukumar samar da abinci ta duniya ta yi kiyasin. Hakan ya ninka adadin tun farkon rikicin, in ji hukumar.

    Hukumar ba da agajin jin kai ta ce ta iya kai muhimman agaji ga kashi 10% na masu buƙata a yankunan da ake fama da rikici.

  3. Zan ƙara haraji kan kayayyakin China idan aka sake zaɓe na -Trump

    Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai sanya ƙarin haraji kan kayayyakin China idan ya lashe zaɓen sugabancin Amurka da za a yi a watan Nuwamba.

    A wata hira da kafar talabijin ta Fox News, ya ce ƙarin da zai yi kan harajin zai kai kimanin kashi 60 cikin ɗari.

    "Dole ne mu yi hakan," in ji Mista Trump, wanda a halin yanzu shi ne kan gaba a yaƙin neman zama ɗan takarar jam'iyyar Republican,

    Mista Trump na fuskantar tuhume-tuhume da dama da suka haɗa da yunƙurin neman soke sakamakon zaɓen 2020, abin da ya musanta.

    A lokacin shugabancinsa, Mr Trump ya haifar da ƙazamin yaƙin kasuwanci tsakanin manyan ƙasashen duniya biyu da ke da ƙarfin tattalin arziki, tare da sanya haraji kan kayayyakin China na biliyoyin daloli.

    Kalaman na Mista Trump na baya-bayan nan sun ɗan saɓa wa furucinsa na baya game da gabatar da harajin gama-gari na kashi 10 cikin ɗari kan duk wasu kayayyaki da ake shigo da su Amurka.

    A watan da ya gabata Sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen ta bayyana cewar shirin da Mr Trump zai yi na ƙarin kudin haraji zai haifar da karuwar tsadar “kayayyaki iri-iri” ga ‘yankasuwa da ɗaukacin al'ummar Amurka.

  4. Masu garkuwa sun sace fasinjojin bas kan hanyar Abuja

    Wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matafiya a cikin wata motar safa guda biyu da ke kan hayarsu ta zuwa Inele-Eteke Ogugu, a yankin Kogi ta gabas.

    Tuni rudunar yansandan jihar ta Kogi ta tabbatar da faruwar lamarin.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar Williams Ayah ya fitar ta ce baturen 'yansandan yankin da jami'an tsaro na sa kai, da wasu mafarauta na can suna fafutukar ganin sun ceto wadanda aka yi garkuwar da su.

    Ya ce lamarin ya rutsa da motar safa mallakin kamfanin GIG mai cin fasinjoji 12 da wata kirar Sienna mallakin kamfanin sufuri mallakin kamfanin ABC da ke dauke da mutun biyu a ciki. Sai dai daga bisani jami'an tsaron sun ceto direban motar kamfanin na GIG, a cewar mai magana da yawun rudunar 'yansandan.

  5. Ba mu ne muka yi sanadin kaɗe saurayi da mota a Jibiya ba - Kwastam

    Hukumar kwastam ta Najeriya ta yi bayani kan batun kashe wani matashi da aka yi a garin Jibiya na jihar Katsina, bayan da aka zargi jami'anta da bin mai motar da gudu a cikin gari.

    A makon da ya gabata ne wasu rahotanni suka ce jami'an hukumar ta kwastam sun bi wani mai mota ƙirar J5 da nufin kama shi, lamarin da ya sanya ya kaɗe wani matashi, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.

    A cikin wata sanarwa da hukumar kwastam ta Najeriya ta fitar, yau Litinin ta hannun jami'in hulɗa da jama'a na rundunar na ƙasa, Abdullahi Maiwada, hukumar ta ce yana da kyau ta fayyace wa al'umma cewa "ba jami'anmu ne suka tuƙa motar ƙirar J5 ba kuma ba su kama motar ba."

    Sanarwar ta ƙara da cewa binciken da hukumar ta gabatar ya nuna cewa direban J5 ɗin na ɗauke ne da waken soya, kuma tuni aka kama shi inda yake hannun jami'an ƴansanda.

    Sai dai sanarwar ta ce hukumar ta kwastam na jajanta wa iyalan mamacin.

    Rahotannin da kafafen yaɗa labaru suka fitar sun ce a ranar Asabar ne wani matashi mai suna Muhsin Ibrahim mai shekara 14 da haihuwa ya rasa ransa bayan da wata mota ƙirar J5 ta kaɗe shi a cikin garin Jibiya na jihar Katsina, wadda ake zargin wasu jami'an kwastam ne suka biyo shi.

    Wannan ba shi ne karon farko da ake zargin jami'an hukumar kwastam da haddasa hatsari ba a garin na Jibiya wanda ke maƙwaftaka da Jamhuriyar Nijar mai maƙwaftaka da Najeriya.

  6. Murar tsuntsaye ta ɓarke a birnin Yamai

    An bayyana cewa murar tsuntsaye ta ɓarke a Yamai, babban birnin Jamhuriyar Nijar bayan da aka gano tsuntsaye da dama na ɗauke da cutar nau'in H5N1.

    Ƙwayar cutar na iya haifar da cuta mai hatsari ga rayuwa a tsuntsaye kamar kajin gida da kuma tsuntsayen daji.

    Mutanen da suke yawan hulɗa da tsuntsayen da ke ɗauke da ƙwayar za su iya kamuwa da cutar.

    Alamomin kamuwa da cutar sun haɗa da zazzaɓi da ciwon jiki da ciwon kai da tari da kuma numfashi sama-sama.

    Hanyoyin kare kai daga cutar sun haɗa da:

    • Wanke hannu da sabulu da ruwa mai gudana ko kuma amfani da sanadarin tsaftace hannu.
    • Ware ɗanyen nama daban da wanda aka dafa za a ci.
    • Dafa nama ya dahu sosai tare da yin taka-tsantsan wajen adana ɗanyen nama.

    Bayanai sun ce an samu ɓarkewar cutar sau da dama cikin shekarun da suka gabata a ƙasar ta Nijar.

  7. Sarki Charles III na Birtaniya na fama da cutar kansa

    Fadar masarautar Birtaniya ta Buckingham ta bayyana cewa an gano Sarki Charles na fama da cutar kansa.

    Sai dai ba a bayyana takamaiman nau'in cutar kansar da aka gano Sarkin na fama da ita ba.

    Amma sanarwar da fadar ta fitar ta bayyana cewa Sarkin zai fara karɓar magani daga ranar Litinin.

    Sanarwar ta ƙara da cewa sarkin "na cike da kyakkyawar fata game da maganin da zai riƙa karɓa kuma yana sa ran komawa aiki kamar yadda ya saba da zarar damar hakan ta samu."

    A yanzu Sarkin zai jingine ayyukansa kuma ana sa ran sauran manyan ƴan gidan sarautar za su gudanar da wasu daga cikin ayyukan yayin da yake karɓar magani.

    Babu dai wani cikakken bayani game da matsayin cutar ta kansa da yake fama da ita.

    Duk da zai jingine ayyukan nasa amma Sarkin zai ci gaba da riƙe muƙamin da kundin tsarin mulki ya ba shi na shugaban gwamnati, ciki har da sanya hannu kan takardu da kuma tattaunawa ta sirri.

    Kimanin mako ɗaya da ya gabata ne aka yi wa Sarkin aiki kan lalurar mafitsara a wani asibiti da ke birnin Landan.

  8. Ƴansanda sun kama 'masu garkuwa da mutane' a Abuja

    Rundunar ƴansandan Najeriya a Abuja, babban birnin ƙasar ta ce ta kama wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutanen ne domin neman kuɗin fansa a wani yanki na birnin.

    A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun mai taimaka mata kan hulda da jama'a, Josephine Adeh, rundunar ta ce ta samu nasarar hakan ne a wani samame da ta kai a wani Otal da ke ƙauyen Bassa, bayan samun wasu bayanan sirri.

    Abuja, babban birnin Najeriya na fuskantar matsalar tsaro a cikin watanni na baya-bayan nan.

    Matsalar garkuwa da mutane da kashe-kashe na ƙara ƙamari, lamarin da ke janyo suka daga ɓangarori da dama.

    Cikin sanarwar, rundunar ta bayyana sunan wasu matasa maza guda huɗu da mata biyu, waɗanda ta ce a cikin su akwai waɗanda suka yi ƙaurin suna wurin satar al'umma.

    Sanarwar ta ƙara da cewa kayan da aka samu a hannun waɗanda aka kama sun haɗa da bindiga ƙirar AK47 guda ɗaya da wayoyin hannu 10 da kuɗi naira 345,000.

  9. Ƴansanda sun jefa wa masu zanga-zanga hayaƙi mai sa hawaye a Senegal

    Jami'an tsaro a Senegal sun jefa wa masu zanga-zanga a ƙofar Majalisar dokokin ƙasar hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa mutanen da suka taru domin nuna adawa da ɗage zaɓen shugaban ƙasar da aka tsara yi ranar 25 ga wannan wata.

    Magoya bayan jam'iyyun adawa sun yi aniyar gudanar da wata gagarumar zanga-zanga ce a gaban ginin majalisar dokokin, sai dai jami'an ƴansanda sun tarwatsa su tare da kama wasu.

    Hakan ya faru ne jim kaɗan gabanin fara muhawara a zauren majalisar game da ƙudurin ɗage zaɓen shugaban ƙasar zuwa ranar 25 ga watan Agustan 2024.

    Kamfanin dillancin labaru na AFP ya ruwaito wasu daga cikin masu zanga-zangar na furta kalaman "Macky Sall ɗan kama-karya" yayin da aka tarwatsa su.

    Ƴan takara na jam'iyyun hamayya sun yi tir da matakin ɗage lokacin zaɓen, inda suka bayyana shi a matsayin 'juyin mulki ga kundin tsarin mulkin ƙasar.'

    Sannan sun yi kira da a gudanar da zanag-zanga a faɗin ƙasar kuma a tabbatar an yi zaɓen a lokacin da aka tsara tun da farko.

    An dai katse sadarwar waya da intanet sannan an dakatar da wani gidan talabijin mai zaman kansa.

    Senegal ta shiga hali na tangal-tangal tun bayan da shugaban ƙasar Macky Sall a ranar Asabar ya sanar da cewa za a ɗage yin zaɓen ƙasar, awanni kaɗan kafin fara yaƙin neman zaɓe a hukumance, lamarin da ya haifar da zanga-zanga a ranar Lahadi.

  10. Hedikwatar tsaron Najeriya ta gargadi kungiyar HURIWA kan rikicin Filato

    Hedikwatar tsaro ta Najeriya, ta ja hankalin kungiyoyi masu kokarin ta'azzara al'amura a daidai lokacin da sojojin suke iya bakin kokarinsu dangane da samar da zaman lafiya yankin da ke fama da rikici a jihar Filato.

    Wannan dai na dauke a cikin wata sanarwa da hedikwatar ta fitar mai sa hannun darektan yada labaranta, Burgediya Janar Tukur Gusau ranar Litinin din nan a Abuja.

    Birgediya General Gusau dai ya maryar da martani ne ga kungiyar HURIWA ta marubuta masu rajin kare hakkin bil'adama wadda ta soki kwamitin da aka kafa domin samo bakin zaren rikicin da ya dabaibaye yankin na jihar Filato.

    Ya ce kwamitin wanda babban hafsan sojojin kasar ya kafa da kansa na karkashin jagorancin tsohon babban soja mai tarin kwarewa.

    Kugiyar ta HURIWA dai a wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi ta hannun shugabanta na kasa, Emmanuel Onwubiko, ta soki babban hafsan sojin kasar inda ta ce ba da gaske yake yi ba wajen warware rikicin na jihar Filato.

  11. Burkina Faso ta fara allurar rigakafin zazzabin cizon sauro

    Burkina Faso yanzu ta gudanar da rigakafin zazzabin cizon sauro da Hukumar Lafiya ta Duniya ta ba da shawara a cikin tsarin rigakafinta na yau da kullun.

    Hakan na nufin cewa jariran da ke ziyartar cibiyoyin kiwon lafiya domin gudanar da allurar rigakafin cutar zazzabin cizon sauro a kasar da ke yammacin Afirka a halin yanzu, za su iya samun maganin zazzabin cizon sauro a matsayin karin kariya daga cutar.

    An yi wa jarirai kusan 250,000 ƴan watanni biyar zuwa shekara guda kashi na farko na wannan allurar rigakafin a gundumomin lafiya 27 da zazzabin cizon sauro ya fi shafa.

    Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce a kowace shekara mutane 600,000 ne ke mutuwa sakamakon zazzabin cizon sauro a Afirka.

    Yara ‘yan kasa da shekaru biyar su ne a kalla kashi 80 cikin 100 na wadanda suka mutu.

    A watan da ya gabata, Kamaru ta zama kasa ta farko a duniya da ta fitar da wannan rigakafin a cikin shirinta na rigakafin yau da kullun.

  12. Namibiya ta fara zaman makoki na kasa bayan mutuwar shugaba Geingob

    Sabon shugaban ƙasar Namibiya, Nangolo Mbumba ya ayyana zaman makoki na kasa domin girmama magabacinsa Hage Geingob, wanda ya rasu a ranar Lahadi.

    Geingob, mai shekaru 82, ya mutu ne a lokacin da yake jinyar cutar daji a wani asibiti da ke Windhoek, babban birnin kasar.

    An fara zaman makoki na ƙasar ne a yau, Litinin kuma zai ci gaba da kasancewa har zuwa ranar da za a yi jana'izar Geingob, wanda har yanzu ba a tantance ba, in ji Ministan ICT Peya Mushelenga a wani jawabi da ya yi wa jama'a.

    "Shugaban kasa ya kafa wani kwamiti ƙarƙashin jagorancin firaminista, wanda ke gudanar da shirye-shiryen jana'izar.

    Wannan kwamitin ne zai ba da sanarwa kan jana'izar " in ji Mista Mushelenga.

    Za a kwantar da dukkan tutocin ƙasar Namibiya da ofisoshin diflomasiyyarta na ketare har zuwa lokacin jana'izar marigayi shugaban kasar.

    Gwamnati ta musanta rahotannin da ke cewa makarantu za su rufe a wannan lokaci.

  13. Mai shekara 72 ta zama mataimakiyar shugaban kasa ta farko a Namibia

    An samu mace ta farko a matsayin mataimakiyar shugaban kasa a Namibia.

    Sabon shugaban Namibia, Nangolo Mbumba wanda ya gaji marigayi shugaba Hage Geingob ne ya sanar da Netumbo Nandi-Ndaitwah, mai shekara 72 a matsayin mataimakiyarsa.

    Netumbo Nandi-Ndaitwah ta dade a fagen siyasar kasar.

    A cewar wani shafin intanet na majalisar dokokin Namibia, an haifi Netumbo Nandi-Ndaitwah ranar 29 ga watan Oktoban 1952 a Onamutai da ke yankin Oshana.

    Ta yi digiri na biyu a ilimin diflomasiyya. Yar siyasa ce da ta rike mukaman siyasa daban-daban musamman a jam'iyyarsu.

    Ta zama 'yar majalisar dokoki sau bakwai daga 1995.

    Ta rike mukamai da dama a kasar ta Namibia daga ciki mataimakiyar ministar harkokin waje da ministar yada labarai. Ta kuma rike ministar walwalar mata da yara sai ministar muhalli da yawon bude ido.

    Ita ce ministar harkokin waje da mataimakiyar Firaiminista kan al'amuran kasa da kasa tun 2015.

  14. An katse sadarwar intanet a Senegal bayan barkewar zanga-zanga

    Gwamnatin Senegal ta sanar da katse hanyoyin intanet na wani dan lokaci a kasar, kwana daya bayan daruruwan mutane sun yi zanga-zangar adawa da matakin Shugaba Macky Sall na dage zaben shugaban kasa.

    Gwamnatin ta ce matakin ya zama dole domin dakatar da yada sakonnin kiyayya da na tada rikici a shafukan sada zumunta kam,ar yadda ministan sadarwa, Moussa Bocar Thiam ya fada.

    Lamarin ya zo kwana daya bayan da yan Senegal suka far wa wani gidan Talabijin kan zargin yana tada husuma a yadda yake bayar da rahotanni kan zanga-zangar.

    A yau ne yan majalisar kasar za su tafka muhawara kan wani kuduri da ke ba da shawarar a yi zaben shugaban kasa ranar 25 ga watan Agusta tare da kyale Shugaba Sall kan kujerarsa har sai an samu magajinsa. Tun farko an tsara yin zaben a ranar 25 ga watan nan na Fabarairu.

    An shirya yin zanga-zanga a wajen majalisar dokokin kasar yau Litinin karkashin maudu'in #FreeSenegal a shafin X.

    Tsohuwar Fraiminista kuma yar takara ta bangaren hamayya, Aminata Toure wadda aka kama a zanga-zangar ranar Lahadi, ta tabbatar cewa an sake ta a wani sako da ta wallafa a intanet.

    • Halin da aka shiga a Gaza ranar da aka katse hanyoyin sadarwa
    • Koriya Ta Arewa ta katse hanyoyin sadarwa tsakanin ta da Koriya Ta Kudu
  15. Najeriya ce kasa mafi sauƙin rayuwa a Afirka – Fadar shugaban Najeriya

    Ofishin shugaban Najeriya ya tayar da kura da iƙirarin da ya yi na cewa kasar ta fi ƙarancin tsadar rayuwa a nahiyar Afirka.

    Mai bai wa shugaban kasa shawara ta musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ne ya fadi hakan a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da yake yin watsi da sukar da Atiku Abubakar ya yi cewa manufofin tattalin arzikin shugaba Bola Tinubu na ƙara jefa ‘yan Najeriya cikin wahala.

    Mista Onanuga ya bayyana wani nazari da wani kamfani intanet Numbeo ya yi kan matsayin Najeriya a tsarin tsadar rayuwa.

    Ya ce cibiyar tattara bayana ta Numbeo ta ce Najeriya ce ke da maki mafi girma wajen samun araha.

    Amma hakan ba ya cikin dukkan ƙasashe 54 na Afirka, domin kasashe 23 ne kawai a nahiyar aka gudanar da binciken a kansu.

    Matsayin Najeriyar zai iya yi wa 'yan kasar dadi kadan - wadanda ke fama da hauhawar farashin kayayyakin abinci da kayan masarufi, da asarar tallafin man fetur, da kuma karancin kudi.

    • Ƙarin hauhawar farashin da aka daɗe ba a gani ba na gigita ƴan Najeriya
    • ‘Matsin rayuwa ya tursasa mini sakin uwargidata don samun saukin dawainiya’
  16. Attajiri a Koriya ta Kudu zai bai wa ma'aikatan da suka haihu dala dubu 70

    Wani kamfanin kere-kere a Koriya ta Kudu ya sanar da biyan takuicin fiye da dala dubu saba'in ga kowane jariri da ma'aikatansa suka haifa cikin shekaru biyu da suka gabata.

    Wannan ne tayi mafi girma da wani kamfani mai zaman kansa ya yi domin rage matsalar karancin haihuwa a kasar.

    Shugaban kamfanin na Booyoung Group, Lee Joong-keun ya ce idan ba an samu sauyi a matsalar ba, Koriya ta Kudu za ta iya zama tarihi a shekaru ashirin masu zuwa.

    Ya kuma yi alkawarin biyan makudan kudi ga ma'aikatan da suka haihu nan gaba.

    Mr Lee wanda biloniya ne, an taba samun sa da laifin almundahana da kauracewa biyan haraji sau biyu.

    Ya yi zaman gidan yari sai dai shugaban kasar ya yi masa afuwa a Agustan bara inda kuma aka ba shi damar ci gaba da tafiyar da harkokin kamfaninsa.

    • Wasu mata sun shigar da ƙara saboda rashin basu damar zubar da ciki
    • Albarkar shayar da jariri nonon uwa
  17. An halaka mutum 10 a hari kan ofishin 'yan sanda a Pakistan

    Akalla jami'an 'yan sanda 10 ne suka mutu a wani hari da aka kai kan ofishin 'yan sanda a arewa maso yammacin Pakistan.

    Tashin hankali ya barke gabanin babban zaben kasar da za a yi a makon nan.

    'Yan bindiga sun kai hari ranar Lahadi da daddare inda suka rika jefa gurneti kamar yadda 'yan sanda a yankin Draban da ke Lardin Khyber Pakhtunkhwa suka bayyana.

    An yi musayar wuta ta fiye da sa'a biyu, sakamakon haka mutum tara sun ji rauni.

    Babu tabbaci kan wanda ke da hannu a harin amma yankin ya yi fama da hare-haren da kungiyar Taliban ta Pakistan da sauran kungiyoyin 'yan tawaye ke kai wa kan gine-ginen gwamnati da na jami'an tsaro da farar hula.

    A ranar Larabar da ta gabata ne, aka harbe wani dan takarar majalisar dokoki a wani yanki na Lardin Khyber Pakhtunkhwa.

    A makon da ya wuce kuma a Balochistan, wani lardi a kudu maso yammacin Pakistan, an sake harbe wani dan siyasa a ofishin jam'iyyarsa sannan harim bom bayan wani gangamin siyasa ya hallaka akalla mutum hudu. Kungiyar IS ta dauki nauyin kai harin.

    A makon da ya gabata ne, rundunar sojin kasar ta kashe 'yan bindiga 24 a wani samame na fatattakar masu ta'addanci a Balochistan.

    • Ƴan sandan Najeriya na kokawa kan hare-haren da ake kai musu
    • Mutane na tserewa daga Kidandan a Kaduna
  18. Rikicin ƙarshen mako a yankin Abyei ya yi sanadin mutuwar mutane da dama

    Aƙalla farar hula 37 ne aka kashe tare da sace 18 a sabbin hare-hare a Abyei, yankin da Sudan ta Kudu da Sudan ke takaddama a kai, kamar yadda hukumomi suka bayyana.

    Wannan dai shi ne hari na baya-bayan nan a rikicin da aka kwashe shekaru uku ana gwabzawa a yankin.

    Galibin waɗanda aka kashe a harin na karshen mako mata ne da kananan yara, in ji hukumar wucin gadi ta yankin.

    An ƙona kasuwanni da wuraren zama tare da sace shanu 1,000.

    Ta zargi wasu kungiyoyin matasa biyu ɗauke da makamai daga jihar Warrap a Sudan ta Kudu da kai samame yankin a ranar Asabar da Lahadi tare da kai hare-hare a wasu kauyuka hudu na Abyei.

    Ministan yaɗa labarai, al'adu, matasa da wasanni a gwamnatin Abyei, Bulis Koch Aguar, ya yi alla-wadai da hare-haren tare da yin kira ga gwamnatin ƙasar a Juba da ta magance rikicin Ngok Dinka na Abyei da Twic Dinka na Warrap.

    A makon da ya gabata, wasu kungiyoyin matasa biyu ɗauke da makamai daga jihar Warrap sun kai farmaki a birnin Abyei, inda suka kashe aƙalla mutane 53, ciki har da dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya biyu, a wani lamari mafi muni a yankin da ake takaddama a kai.

    Abyei dai ya kasance yanki ne da ake ta takaddama a kai tsakanin Sudan da Sudan ta Kudu, ganin kawo yanzu ƙasashen biyu ba su warware takaddamar da ke tsakaninsu kan matsayin yankin na karshe ba.

    • 'Sai mun sayar da rai muke zuwa binne matattu a Sudan'
    • Rikicin Sudan: Shugabanni sun ɗauki aniyar kawo ƙarshen rikici
  19. Aiki ya samu Atiku Abubakar – Fadar shugaban Najeriya

    Fadar shugaban kasan Najeriya ta mayar wa da dan takarar shugaban kasar a jam'iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar martani cewa yanzu ya samu abin yi da zai sanya shi ya rinka motsawa tunda ya gaza cimma burinsa na zamowa shugaban Najeriya.

    A wata sanarwa, mai taimaka wa shugaba Tinubu, Bayo Onanuga ya ce Atiku Abubakar na ta koarin mayar da kansa madugun adawa ga shugaba Bola Tinubu da gwamnatinsa.

    Sai dai sanarwar ta ce Atiku Abubakar ya gaza a sukan da yake yi wa gwamnatin saboda irin yadda kalaman nasa dangane da tattalin arziki suke kama da na irin maganganun da ake yi a teburin mai shayi.

    Atiku Abubakar dai ya soki shugaba Tinubu ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi inda ya nuna cewa Tinubu ba zai iya jagoranci ba kuma yana bukatar taimako musamman dangane da abin da ya shafi tattalin arziki.

    Atiku kuma alakanta duk wahalhalu da matsin rayuwar da 'yan kasar ke fama da su ga irin matakan tattalin arzikin da gwamnatin ta Tinubu ta dauka da suka hada da karya darajar naira.

    To sai da mista Bayo Onanuga ya ce "Atiku ba zai zuga 'yan Najeriya ba " kasancewar da ma can shugaba Tinubu ya sanar da su cewa wasu daga cikin matakan da gwamnatin ta dauka ka iya haifar da rashin jin dadi na dan wani lokaci.

    Daga karshen sanarwa ta kara da cewa "Atiku ba zai iya dakatar da ayyukan gyara da gina kasa da gwamnatin shugaba Tinubu ta sanya a gaba ba".

    • Sa'insar Atiku da Tinubu, rufe kasuwannin canji a Abuja da Kano
    • Har yanzu zafin shan kaye ne ke damun Atiku - Tinubu
  20. Yadda mazauna birnin Minna ke zanga-zangar tsadar rayuwa

    Al'umma a Minna, babban birnin jihar Neja na gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Najeriya inda suka rufe manyan titunan da ke birnin.

    Masu zanga-zangar sun hada da mata da matasa inda suke rera wakoki yayin da jami'an tsaro har da yan sanda ke gefe suna kallo.

    Wasu daga cikin masu zanga-zangar sun ce dole ce ta tursasa musu fitowa kan titi domin bayyana halin da suke ciki.

    Wata mace daga cikin masu zanga-zangar ta shaida wa BBC cewa: "Shinkafar da muke ci a baya yanzu ko rabi ba mu iya samu, dubu ɗaya ake sayar da mudu ɗaya, garin masara ma dubu ɗaya da naira ɗari ake sayar da mudu ɗaya."

    Ta ƙara da cewa "aure ma rabuwa yake yi saboda tsadar abinci... wasu mazan ma ba a ƙara ganin su saboda tsadar abinci."

    Mataimakin gwamnan jihar Neja, Yakubu Garba a lokacin da yake yi wa masu zanga-zangar jawabi, ya ce gwamnati tana sane da irin kunci da wahalar da jama'a suke fuskanta a yanzu.

    Ya ce gwamnati tana aiki domin rage halin matsi da aka shiga da kuma tasirin da ake gani sanadin cire tallafin mai.