Shugabannin sojin da ke yaki da juna a Sudan sun sha alwashi ci gaba da gwabza fada, daidai lokacin da ake kokarin shawo kan yankin da ya daidaita kasar.
Manayan janarl din biyu wato Janaral Abdel Fattah al-Burhan da ke jagorantar rundunar sojin Sudan, da Janaral Hamdan Dagalo da aka fi sa ni da Hemete mai jagorantar sojin RSF, sun yi tsokacin a ranar Litinin da ta zamo ta tunawa da shkaru 68 da Sudan ta karbi 'yancin kai.
Hemeti ya ce za su ci gaba da dannawa babu gudu ba ja da baya, za kuma su kawo karshen yakin bayan yin nasara kamar yadda 'yan Sudan suke muradi, da samar da kasar da za ta bai wa dukkan 'yan kasa 'yanci ba tare da nuna wariya ba.
''Sojojinmu za su murkushe sojin gwamnati, mun yi nasara a wurare da dama ciki har da birnin Khartoum, da Darfur, da Kordofan da kuma Jazira,'' in ji Memeti. Ya kuma yi alkawarin kare farar hula musamman a tsakiyar jihar Jazira da anan fadan ya fi zafi a halin yanzu.
Ana sa bangaren shugaba Abdel Fatta al-Burhan, shi ma alwashin ya ci da jaddada nasarar da na su sojojin suka yi, da alkwarin kubutar da Sudan daga abin da ya kira ''hannun masu cin amanar kasa.''
A baya dai ya yi kokarin sasantawa da shugabannin RSF, domin dorewar zaman lafiya a Sudan, sai dai hakan ba ta samu ba lokavcin da RSF suka fara kaddamar da yakin karbe iko da kasar a watan Afirilun shekarar 2023.
Kalaman na su masu zafi na zuwa ne, bayan sun aminta da zaman a teburin sulhu a wannan watan, wanda shi ne karon farko tun bayan barkewar yakin watanni 9 da suka gabata.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane 12,000 aka kashe daga lokacin, ya yin da wasu m,iliyan 6 suka rasa muhallansu.