Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Kotun ƙoli za ta sanar da ranar bayyana hukunci kan zaɓen gwamnan Kano

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba and Haruna Kakangi

  1. Majalisar dokokin Sokoto ta amince a kafa rundunar tsaron al'ummar jihar

    Majalisar dokokin jihar Sokoto ta amince da buƙatar gwamna Ahmed Aliyu na kafa rundunar tsaron al'umma.

    Majalisar ta ɗauki matakin ne bayan amincewa da wani rahoton haɗin gwiwa na kwamatocin majalisar kan tsaro da ayyuka na musamman da shari'a da haƙƙin jama'a.

    Shugaban kwamitin, Alhaji Nasiru Adamu ya ba da rahoton cewa an yi nazari sosai kan ƙudirin inda aka samu shawarwari 28.

    "Waɗan nan shawarwari sun haɗa da sauya sunan ƙudirin zuwa ƙudirin neman kafa rundunar samar da tsaron al'umma ta jihar Sokoto domin samar da zaman lafiya da tsaron rayuka da kuma dukiyoyin al'umma tare da kai ɗauki a lokutan gaggawa," in ji shi.

    Kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Tukur Bala ya gabatar da rahoton domin amincewa inda kuma ƴan majalisar suka amince da buƙatar ta hanyar kaɗa ƙuri'a.

  2. MDD ta dakatar da taimakon abinci a birnin Sudan da RSF ta ƙwace

    Hukumar samar da abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta dakatar da kai kayyakin abinci zuwa jihar Gezira na wani ɗan lokaci, kwanaki bayan da dakarun RSF suka ƙwace iko da birnin Wada Madani.

    Shugaban hukumar WFP a Sudan, Eddie Rowe cikin wata sanarwa a ranar Laraba, ya ce wajen mafaka a yanzu ya zama fagen daga lamarin da yake da mummunan tasiri a kan farar hula.

    "Hakan ya tilasta WFP tsagaita shigar da kayayyakin abinci zuwa wasu wurare a jiharGezira daidai lokacin da mutane suka fi bukatar agaji."

    An yi ƙiyasin mutum 300,000 ne suka tsere wa rikici a jihar tun Juma'ar da ta gabata, kamar yadda hukumar ta bayyana.

    WFP ta daɗe tana samar da agajin abinci ga mutum 800,000 a Gezira da waɗanda suka ɗaiɗaita sakamakon yaƙi a Khartoum, babban birnin Sudan.

    Akwai fargabar soma yaƙi a Gezira na iya ta'azzara matsalar jin ƙai a Sudan.

    • 'An aikata kisan ƙare-dangi a Darfur'
    • 'Sai mun sayar da rai muke zuwa binne matattu a Sudan'
  3. Kotun ƙoli za ta yi zaman sauraron ƙara kan zaɓen gwamnan Kano

    Gaba a yau Alhamis ne ake sa ran Kotun ƙolin ƙasar za ta fara sauraron ɗaukaka ƙarar da gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf da jam'iyyarsa ta NNPP suka shigar a gabanta.

    Gwamnan na jam'iyyar NNPP na ƙalubalantar hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da ya tabbatar da hukuncin kotun sauraran ƙararrakin zaɓe da ta soke nasararsa tare da bayyana Nasiru Gawuna na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar.

    Wannan ne dai karon farko da kotun za ta fara zama kan ƙarar da gwamnan ya shigar.

    Ɗaya daga cikin lauyoyin NNPP, Barista Bashir Muhammad Tudun Wuzirci ya ce sun gabatar da dukkan abubuwan da ya kamata su gabatar gaban kotu.

    "Da yardar Allah kotu za ta tabbatar da zaɓn da mutanen Kano suka yi wa Abba Kabir Yusuf." kamar yadda Barista Bashir Tudun Wuzurci ya bayyana.

    A nasa ɓangaren. lauyan APC, Barista Abdullahi Adamu Fagge ya ce "dukkan ɓangarorin biyu musamman su waɗanda suka ɗaukaka ƙara za su yi bayani na cewa kotun ƙasa ta yi kuskure ba ta yi daidai ba dangane da hukuncin da ta yi,"

    "Daga ɓangarenmu mu da aka ɗaukaka ƙara a kan hukuncin da ya yi mana daɗi, za mu yi bayanai mu nuna cewa hukuncin nan an yi shi daidai, kotun ɗaukaka ƙara ta yi daidai, muma mu zo da hujjoji gamsassu na shari'a." in ji lauyan APC.

    Suma masu ruwa da tsaki a jam'iyyun NNPP da APC suna ji gaba da yin tsokaci kan lamarin. Hisham Habib, ɗan jam'iyyar NNPP ya yi fatan kotun ta duba wahalar da mutanen Kano suka sha ta yi watsi da tsarin da aka zo da shi da ake ganin ba shi da tasiri.

    Suma ƴan jam'iyyar APC kamar Aminu Mi Dawa Fagge ya ce suna ci gaba da addu'ar nasara kuma sun nemi jama'ar Kano su karɓi kowane hukunci kotu za ta yanke domin zaman lafiya da kuma ci gaban jihar.

    • Kotun ɗaukaka ƙara ta kammala sauraron shari'ar zaɓen gwamnan Kano
    • Siyasar Kano: APC da NNPP sun koma ga Allah kafin hukuncin kotu
  4. Barka da safiya!

    Masu bibiyar mu a wannan shafi na Kai Tsaye, barkanmu da warhaka. Da fatan mun wayi gari cikin ƙoshin lafiya.

    Kamar yadda aka saba, za mu wallafa muku labarai da rahotanni game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Akwai ƙarin labarai har ma da bidiyo a shafukanmu na sada zumunta - Facebook da X (Tuwita) da ma Instagram.

    Nabeela Mukhtar Uba tare da Haruna Ibrahim Kakangi za mu kasance da ku har zuwa lokacin da za mu miƙa ragama ga sauran abokan aiki.