Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Al'ummar Congo na zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisu

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Haruna Kakangi and Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Blinken ya mai da martani kan sukar da ake yi wa Amurka kan Isra'ila

    A wani taron manema labarai na ƙarshen shekara, sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken mayar da martani kan sukar da ake yi wa Amurka yaƙin da Isra'ila ke gudanarwa a Gaza.

    Yana magana ne a yayin da jami'an diflomasiyyar Majalisar Ɗinkin Duniya ke yunƙurin gujewa sake ƙin amincewa daga Amurka kan ƙudurin tsagaita wuta a Gaza.

    "Ba na jin wani yana kira ga Hamas ta daina fakewa da fararen hula, ta ajiye makamanta, ta kuma mika wuya," in ji shi. "Komai zai ƙare gobe idan hakan ya faru."

    Ya ƙara da cewa, "Yaya zai kasance ba a buƙatar komai daga maharin, sai gabatar da buƙatu ga wanda aka azabtar," in ji shi, yana mai jaddada cewa harin Hamas na ranar 7 ga Oktoba ne musababbin yaƙin.

    Blinken ya ce Amurka ta kasance kan gaba wajen kai agajin jin ƙai a Gaza kuma tana son tabbatar da cewa ƙudurin Majalisar Ɗinkin Duniya ya ci gaba da kokarin… ba tare da al'amura sun sake taɓarɓarewa ba.

    Ya sake nanata matsayin gwamnatin na cewa dole ne Isra'ila ta ƙara yin ƙoƙarin kare fararen hula, amma tana da hakkin gudanar da wannan yaƙin.

    Ofishin yaɗa labarai na gwamnatin Hamas ya sanar da cewa adadin mutanen da Isra'ila ta kashe a Gaza a yanzu ya zarce 20,000.

  2. Tinubu ya buƙaci a tantance mutane 11 a matsayin alkalan kotun ƙoli

    Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci majalisar dattawa ta tabbatar da mutane 11 da za a naɗa a matsayin alƙalan kotun ƙolin Najeriya.

    Shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ya karanta wasiƙar shugaban ƙasar a zauren majalisar a ranar Laraba.

    Don haka kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin shari’a ya fara tantance sunayen mutane 11 da majalisar shari’a ta ƙasa ta miƙa.

    Daga cikin wadanɗa za a tantance akwai mai shari’a Haruna Tsammani, wanda ya jagoranci kotun sauraron ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

    Sauran alƙalan sun haɗa da:

    Hon. Justice Jummai Hannatu Sankey, OFRHon. Justice Chidiebere Nwaoma UwaHon. Justice Chioma Egondu Nwosu-IhemeHon. Justice Moore Aseimo A. AdumeinHon. Justice Obande Festus OgbuinyaHon. Justice Stephen Jonah AdahHon. Justice Habeeb Adewale O. AbiruHon. Justice Jamilu Yammama TukurHon. Justice Abubakar Sadiq UmarHon. Justice Mohammed Baba Idris

    Idan aka tantace alƙalan, kotun ƙolin za ta kasance tana da alƙalai 21, kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada.

  3. Bankin raya ƙasashen Afirika zai janye ma'aikatan ƙasashen waje daga Ethiopia

    Bankin raya ƙasashen Afirika zai janye duka ma'aikatansa 'yan ƙasashen waje daga Habasha bayan cin zarafin ma'aikatansa da jami'an tsaron ƙasar suka yi.

    A watan da ya gabata bankin ya yi shigar gaban hukumomin ƙasar tare da bayanin cin zarafi da kuma tsare biyu daga cikin ma'aikatansu na wasu sa'o'i a matsayin babbar matsala ta diflomasiyya.

    Lamarin ya faru ne a ranar 31 ga watan Oktoba.

    Ministan harkokin kuɗin Habasha Eyob Tekalign yace gwamnati tayi nadamar afkuwar lamarin

    Bankin wanda ke da hedikwata a Ivory Coast na ɗaya daga cikin manyan hukumomin da suke ƙoƙarin samar da cigaba a Afirika.

    Bankin na samar da kuɗi ga hukumomin gwanmati da kuma kamfanoni masu zaman kansu wanda hakan ke kawo cigaba a nahiyar.

    Bankin yana da ayyukan da suka kai 22 da yake yi a habasha da ƙimarsu zata kai dala biliyan 1.2 a cewar bankin.

  4. Malaysia ta haramta wa jiragen dakon kaya na Isra'ila shiga tashar ruwanta

    Malaysia ta sanar da cewa ta haramta wa jiragen dakon kaya masu ɗauke da tutar ƙasar Isra'ila shiga tasoshin ruwanta.

    Cikin wata sanarwa da ya fitar, Firaministan Malaysia Anwar Ibrahim ya ce an janye izinin da aka bai wa ZIM, babban kamfanin jigilar kaya na Isra'ila na yin amfani da tashar jiragen ruwan Malaysia sakamakon keta haƙoƙin ɗan'adam da ake yi a Gaza.

    An hana duka jiragen ruwa da ke kan hanyar zuwa Isra'ila ɗaukar kaya a tashar jiragen ruwa ta Malaysia.

    Akasarin al'ummar Malaysia Musulimi ne kuma ƙasar ba ta da alaƙar diflomassiya da Isra'ila, yayin da gwamnatin ƙasar ta sha matsin lamba daga cikin gida kan aiwatar da wannan haramcin.

    Mahukuntan kamfanin Zim da jami'an gwamnatin Isra'ila ba su mayar da martani kan lamarin ba zuwa yanzu.

  5. Amurka na iya ƙin amincewa da ƙudirin tsagaita wuta a Gaza

    Ana ci gaba da jinkirta kaɗa ƙuri'a a kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) kan tsagaita wuta a Gaza domin kuace wa rashin amincewa daga Amurka.

    Hadaddiyar Daular Larabawa ta so ta gabatar da daftarin ƙudirinta ga kwamitin tun ranar Lahadi, amma a cikin kwanakin da suka gabata lamarin na ta kwam-gaba kwan-baya

    Tattaunawar ta ci gaba har cikin dare a ranar Talata.

    An yi sauye-sauye da dama kan daftarin don shawo kan Amurka, amma a ƙarshe an ce Washington na adawa da kafa wani shiri na MDD na sa ido kan agaji a Gaza.

    Yanzu haka mambobin kwamitin tsaron sun fara tunanin cewa Amurka na iya ƙin amincewa da ƙudirin karo na uku domin daƙile matakin majalisar kan yaƙin Isra'ila da Hamas.

    Amurka ba ta fito fili ta bayyana yadda za ta kaɗa ƙuri’a ba, ita ma Birtaniya ba ta bayyana ba, amma BBC ta fahimci daftarin zai samu gagarumin goyon baya a majalisar.

  6. Yadda za ku tantance gurɓataccen lemo da sauran abubuwan sha a Najeriya

  7. Shugaba Tinubu ya rage rabin kuɗin mota ga matafiya a Najeriya

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da rage kuɗin sufuri ga ‘yan Najeriya da kashi 50 cikin 100.

    Ministan ma’adanai na ƙasa, Dele Alake, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai ranar Laraba kan tallafin shugaban ƙasa a harkokin sufurin jama’a domin murnar bikin Kirsimeti a Abuja.

    A cewar Alake, tallafin zai fara ne a ranar Alhamis, 21 ga watan Disamba, kuma zai ƙare a ranar 4 ga Janairun 2024.

    “Abin da hakan ke nufi shi ne, daga gobe [Alhamis], ‘yan Nijeriya masu son yin balaguro za su iya hawa motocin haya na kamfani a kan rangwamen kashi 50% na farashin da ake kashewa a halin yanzu, da kuma duk tafiyar da za a yi a kan hanyoyin jiragen kasa a halin yanzu ba tare da sun biya kuɗi ba a wannan lokacin na hutu.” in ji shi.

    Ya yi bayanin cewa Shugaba Tinubu ya amince da hakan ne domin nuna soyayyarsa ga ‘yan Najeriya, inda ya ƙara da cewa matakin ya bai wa ‘yan Najeriya da ke son yin balaguro don ziyartar ‘yan uwansu da garuruwansu damar yin hakan ba tare da damuwa ba yayin da tsadar rayuwa ke ƙamari a wannan lokacin.

    Alake ya bayyana cewa Tinubu ya umurci ‘yan sanda da hukumar DSS da sojoji da sauran jami’an tsaro su haɗa kai don ganin an gudanar da bukukuwan lafiya ba tare da taɓarɓarewar tsaro a kowane bangaren ƙasar ba.

  8. A shirye muke mu sake tsagaita wuta, in ji Shugaban Isra'ila Herzog

    Shugaban Ƙasar Isra'ila, Isaac Herzog, ya ce ƙasar a shirye take ta sake dakatar da bude wuta domin ganin an sako wasu ƙarin mutanen da ake garkuwa da su a yankin da kuma kai kayan agajin da ake bukata.

    Gwamnatin Isra'ila na fuskantar matsin lamba daga ƙasashen duniya kan amincewa da tsagaita wuta a daidai lokacin da ake ci gaba da samun asarar rayukan fararen hula da kuma mummunan rikicin jin-kai a Gaza.

    Har a cikin gida ma gwamnatin na fuskantar matsin lamba kan yarjejeniyar sakin wasu da ake garkuwa da su bayan da sojojin Isra'ila suka kashe wasu Isra'ilawa uku da Hamas ta yi garkuwa da su bisa kuskure a makon jiya.

    Kalaman Herzog na zuwa ne a daidai lokacin da kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ke shirin kaɗa ƙuri'a kan wani sabon kudiri na neman tsagaita wuta a Gaza.

    A watan da ya gabata ne wata yarjejeniya tsakanin Isra'ila da Hamas da wasu masu shiga tsakani na ƙasashen waje suka kulla ta kai ga dakatar da buɗe wuta na wani ɗan lokaci tare da sako wasu mutane kusan 100 da aka yi garkuwa da su. A madadin haka, Isra'ila ta sako Falasdinawa da take tsare da su a gidajen yarinta.

    Kawo yanzu mahukuntan Isra'ila sun yi watsi da batun sabuwar yarjejeniyar tsagaita wutar, suna masu cewa ƙungiyar Hamas ce kawai za ta amfana.

    Hamas kuma ta ce duk wata tattaunawa ta musayar fursunoni za ta faru ne bayan an dakatar da kai hare-hare a Gaza.

  9. An rantsar da Simon Lalong a matsayin sanata

    An rantsar da tsohon gwamnan jihar Filato, Simon Lalong, a matsayin ɗan majalisar dattijai mai wakiltar mazaɓar Filato ta Kudu.

    An rantsar da shi ne a lokacin zaman zauren majalisar na ranar Laraba.

    Hakan na zuwa ne bayan Lalong ya ajiye muƙaminsa na ministan ƙwadago a gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

    A wata wasiƙa da ya gabatar wa shugaban ƙasa a ranar Talata, ministan ya tunatar da shugaban ƙasar cewa kotun ɗaukaƙa ƙara ta bayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen sanata mai wakiltar Mazabar Filato ta Kudu tare da bayar da umarni ga hukumar zaɓe INEC ta miƙa masa shaidar nasarar cin zaɓe.

    Lalong ya ce bai yanke shawarar murabus daga minista cikin hanzari ba saboda amanar da shugaban ƙasa ya damƙa masa a matsayin minista a majalisar zartarwa bayan ya rike mukamin darakta janar na kwamitin yaƙin neman zaben jam’iyyar APC.

  10. Dalibai sun shigar da ƙara bayan an rage daƙiƙa 90 cikin lokacin jarabawa

    Wasu ɗaliban koriya ta kudu sun shigar ƙara kan gwamnati bisa tuhumar tsayar da jarabawar shiga kwaleji daƙiƙa 90 kafin lokacin da aka tsara musu

    Sun buƙaci a biya kowannensu dala15,400 , wanda shi ne kuɗin karatun sake ɗaukar jarabaewar

    kuskuren ya shafi jarabawar sauran ɗaliban a cewar lauya+nsu

    Jarabawar shiga kwaleji ta ƙasa wanda, da ake kira Suneung , jarabawa ce da ake kwashe tsawon awa takwas ana yi ba tare da tsagaitawa ko hutu ba inda a ke rubuta darussa masu yawa.

    Suneung na daya daga cikin jarabawa mafi wahala a duniya

    Amfaninta bai tsaya iya wajen tantance gurbin jami'a da wajen aiki ba, ta na da tasiri akan mu'amalar rayuwa. An saka matakai domin taimakawa daliɓai wajen mai da hankali a lokacin jarabawar da ake yi shekara shekara kamar rufe sararin samaniya da kuma jinkirta buɗe kasuwar hannun jari

    An fitar sakamakon jarabawar na wannan shekarar a ranar 8 ga watan disamba.

    A cikin ƙarar da aƙalla ɗalibai 39 suka shigar a ranar talata, sun yi iƙirarin cewa an buga ƙararrawa a wani wurin gudanar da jarabawar da ke babban birnin ƙasar Seoul a lokacin darasin harshe Korean wanda shine darasin farko a jarabawar.

  11. Ana ƙara hanzari wajen ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

    A yayin da tsagaita wuta a zirin Gaza ya yi kama da abu mai wahala, akwai sababbin alamomi da ke nuni da yiwuwar kawo ƙarshen faɗan tsakanin Isra'ila da Hamas.

    Hakan na nufin sai Hamas ta sauya ra'ayinta na cewa za ta ƙara sakin Isra'ilawa da ta yi garkuwa da su ne kawai idan aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta na dindindin.

    Jagoran ƙungiyar Hamas Ismail Haniyeh ya yi balaguro zuwa birnin Alƙahira na Masar tare da tawagar manyan ƴan ƙungiyar domin tattaunawa da shugaban hukumar leƙen asiri Abbas Kamel. Wannan ya nuna muhimmancin ƙoƙarin tsagaita wutar.

    A bayanan da suka fito daga manyan kafafen labarai na Isra'ila, ƙasar ta gabatar da tsarinta ga masu shiga tsakanin, wanda take neman sakin wasu ƴan isra'ila 30 zuwa 40 da aka yi garkuwa da su.

    Wannan tsarin ya fi bai wa mata fifiko da kuma maza masu shekaru, sai kuma mazan da ke buƙatar kulawar asibiti da hanzari.

  12. Amurka na tunanin ayyana ƴan Houthi a matsayin ƴan ta'adda

    Amurka na duba yiwuwar ayyana ƴan tawayen Houthi da ke Yemen a matsayin ƴan ta'adda.

    Ƴan tawayen waɗanda ke samun goyon bayan Iran na ƙaddamar da hare hare kan jiragen ruwan kasuwanci a tekun maliya a matsayin martani ga yaƙin da Isra'lla ke yi a Gaza.

    Amurka ta ce za ta jagoranci wani ƙawance na ƙasa da ƙasa domin samar da tsaro ga harkokin sufurin jiragen ruwa a tekun.

    Wakilin BBC ya ce ƴan Houthin sun ce ƙawancen da za a samar don kare harkokin jiragen ruwa a tekun maliyan mataki ne na ci gaba da ƙuntata wa Falasdinawa.

  13. Ƴan majalisar Rivers sun janye ƙudirin tsige gwamna Fubara

    Ƴan majalisar dokokin jihar Rivers da suka koma jam'iyyar APC sun janye ƙudirinsu na son tsige gwamna Siminalayi Fubara.

    Ƴan majalisar ƙarƙashin shugaban ɗaya ɓangaren Martin Amaewhule sun janye ƙudirin bayan sun koma zama a yau, Laraba.

    Hakan ya faru ne sakamakon shiga tsakanin da shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yi domin sasanta ɓangarorin biyu.

    Sai dai kwamishinan yaɗa labarai, Joseph Johnson ya musanta masaniya kan hakan.

    Ya faɗa wa jaridar Vanguard cewa gwamnatin jihar ba ta san da wannan batu ba.

    Ƴan majalisar sun ce sun sauya matsayar ne domin mutunta yarjejeniyar da aka cimma domin sasanta rikicin.

    A takardar sanar da janyewar da aka karanta a zauren majalisar, ƴan majalisar sun ce sun ɗauki matakin ne a matsayin girmamawa ga shugaban ƙasa.

  14. Ba za a katse layukan intanet ba lokacin zaɓe – Gwamnatin Congo

    Hukumomi a Jamhuriyar dimokraɗiyyar Congo sun yi alƙawarin ba za a katse sadarwar intanet ba yayin da ake zaɓe a ƙasar.

    Sanarwar ta zo ne sakamakon fargabar da ma'abota shafukan sada zumunta suka nuna game da rashin wuta da kuma maguɗin zaɓe.

    "Ba za mu katse layukan intanet ba saboda ba ma cikin yanayin yaƙi ko tashin hankali," kamar yadda ministan harkokin cikin gida, Peter Kazadi ya bayyana a wani taron ƴan jarida ranar Talata.

    Ya kuma yi gargaɗi cewa za a kama duk wani mai son ta da zaune tsaye ko kawo hargitsi lokacin zaɓen.

    Suma hukumomin sufuri sun sanar da rufe iyakokin tudu da na ruwa tsawon kwana guda.

    A cewar shugaban hukumar shige da fice ta ƙasar, iyakokin za su kasance a rufe har sai ƙarfe 11:59 na dare agogon ƙasar.

  15. Da yawan rumfunan zaɓe a rufe suke – Denis Mukwege

    Ɗan takarar shugaban ƙasa a Congo, Dr Denis Mukwege shi ma ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen da ke gudana a ƙasar.

    Dr Mukwege ya samu rakiyar wasu jami'ai a lokacin da ya yi zaɓe a Kinshasa, babban birnin ƙasar ta Congo.

    Ya kuma koka kan abubuwan da suka faru a wasu mazaɓu da ke sassan ƙasar.

    "Bayanan da muke samu ba su da daɗin ji," in ji Dr Mukwege kamar yadda ya faɗa wa BBC.

    "Akwai rumfunan zaɓe da dama da ba su riga sun buɗe ba. Abin damuwa ne a gare mu amma muna jira mu ga yadda za ta kaya," in ji shi.

    Ɗan takarar na jam'iyyar ACRN ya bayyana ƙudirinsa na fitar da ƙasar Congo daga matsalar yaƙi da yunwa da sauran matsaloli idan ya yi nasara.

  16. Ƴan bindiga sun sace mai shari'ah a jihar Akwa Ibom

    Rundunar ƴan sanda a jihar Akwa Ibom da ke kudancin Najeriya sun ce ƴan bindiga sun yi garkuwa da mai shari'a ta wata babbar kotu tare da kashe jami'in da ke ba ta tsaro.

    Bayanai na cewa an yi garkuwa da Mai shari'a Joy Uwanna a hanyarta ta komawa gida bayan ta tashi daga aiki a kotun da ke kan titin Uyo zuwa Okoboin a garin Oron.

    Ana zargin ƴan bindigar sun buɗe wuta tare da harbin ɗan sandan da ke tare da mai shari'ar kafin daga bisani su yi awon gaba da ita da kuma direbanta.

    Kakakin ƴan sandan jihar, Odiko Macdom ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici inda ya ƙara da cewa jami'an tsaro suna bincike a kai.

    Zuwa yanzu babu wanda ya ɗauki nauyin kai harin amma garkuwa da mutane domin kuɗin fansa da ƴan bindiga ke yi abu ne da ya zama ruwan dare a wasu sassan Najeriya.

  17. Kotu ta haramta wa Trump tsayawa takara

  18. Zaɓen Congo cike yake da hargitsi – Ɗan takarar Jam'iyyar ECIDE

    Ɗaya daga cikin manyan ƴan takarar da ke fafatawa a zaɓen Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo, Martin Fayulu na Jam'iyyar ECIDE ya jefa ƙuri'arsa a La-Gombé da ke tsakiyar Kinshasa, babban birnin ƙasar.

    Tuni dai Fayulu wanda bai yi nasara ba a zaɓen 2018 ya ayyana kansa a matsayin wanda ya fi cancanta ya fitar da ƙasar daga matsalar rashin tsaro.

    "Kun ga yadda ta kaya a duk inda na je, wa ya fi taka rawar gani? Mutane na zuwa su faɗa muku game da rayuwarsu, su faɗi bayanan ƙarya domin janyo hankalin duniya," kamar yadda Martin Fayulu ya shaida wa BBC bayan da ya jefa ƙuri'arsa .

    Fayulu ya kuma soki abin da ya kira rashin tsari ranar zaɓen.

    Ya ce "ina da jama'ata da ke rangadi a duk faɗin ƙasar. A Kaluka, babu komai, sai ma ka je can. Akwai wuraren da ba su da kayan aiki a Boumbo yana mai bayyana cewa komai a hargitse yake a ranar zaɓen nan.

    Ya zargi Mr Kadima da shirya hargitsin amma a cewarsa, hukumar zaɓe ta CENI ta ce akwai cibiyoyin zaɓe fiye da 71,000. Ya zama dole a ƙyale mutane su yi zaɓe a rumfunan," kamar yadda ya yi fata.

  19. Shugaban Hamas ya isa Alƙahira don tattaunawa kan tsagaita wuta a Gaza, Yolanda Knell daga Gabas ta Tsakiya

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da rahoton cewa shugaban Hamas Ismail Haniyeh ya isa birnin Alƙahira domin tattaunawa da hukumomin Masar kan tsagaita wuta a Gaza.

    Isra'ila ta bayyana cewa a shirye take ta amince da dakatar da yaƙi domin ƙara sako mutanenta da ake garkuwa da su.

    Masar tare da Qatar sun taimaka wajen cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta mako ɗaya a watan da ya gabata wadda ta yi sanadiyyar sako ƴan isra'ila 100 waɗanda Hamas ta yi garkuwa da su yayin da Isra'ila ta sako Falasɗinawa 240 da take rike da su a gidajen yari.

    Ana sa ran Ismail Haniyeh, wanda yake zama a Qatar zai jagoranci tawagar manyen ƴan ƙungiyar ta Hamas zuwa Masar domin ganawa da shugaban hukumar leƙen asirin ƙasar.

    Shugaban Isra'ila Issac Herzog ya ce ƙasarsa a shirye take ta tsagaita wuta domin ba da damar sako ƙarin ƴan isra'ilan da ake garkuwa da su.

    A daren jiya. Talata ne mayaƙan ƙungiyar Falasɗinawa ta Palestinian Islamic Jihad (PIJ), da ke da kusanci da Hamas suka saki sabon bidiyo da yake nuna ƴan Isra'ila biyu - Gadi Moses ɗan shekara 79 da kuma Elad Katzir ɗan shekara 47 da Hamas ta yi garkuwa da su suna roƙon a sake su su koma gida.

    Ƙasashen duniya na ci gaba da matsawa kan ƙara tsagaita faɗan domin samun damar ƙara shigar da kayayyakin agaji cikin Gaza.

  20. 'Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 100 a Deir al-Balah'

    Ma'aikatar lafiya ta Hamas da ke Gaza ta ce an kashe Falasɗinawa 100 a hare-haren da Isra'ila ta kai a yankin ranar talata.

    Hotuna daga Deir-al-Balah, wani birni da ke tsakiyar Gaza sun nuna Falasɗinawa lulluɓe da ƙura tsaye cikin ɓuraguzon gine-ginen da suka rushe.