A cikin 'yan sa'o'i da suka gabata mun sami rahotannin ci gaba da kai hare-haren bama-bamai da fada a Gaza, da kuma hare-hare a Gaɓr Yamma da Kogin Jordan.
A kudancin Gaza, Isra'ila na kai hare-hare ta sama kan birnin Rafah, a cewar kamfanin dillancin labaran Falasɗinawa Wafa
A Khan Younis, inda dubban ɗaruruwan mutanen Gaza suka nemi mafaka, tankunan Isra'ila sun yi ta tahowa zuwa tsakiyar birnin.
Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, mayaƙan masu iƙirarin jihadi sun tarwatsa wani gida a Khan Younis inda sojojin Isra'ila ke neman wani hanyar ƙarƙashin ƙasa. A cikin sa'o'i na karshe rundunar ta ce sojojinta da dama sun samu munanan raunuka a kudancin Gaza.
Har ila yau Isra'ila na ci gaba da kai hare-hare a yankunan arewacin yankin, inda sojojin suka ce sun kewaye yankunan karshe na Hamas a Jabaliya da Shejaiya.
Kafofin yaɗa labaran Falasɗinawa sun kuma bayar da rahoton samame tare da kame a wasu garuruwan da ke Gaɓar yamma da Kogin Jordan cikin dare.
Hotunan da cibiyar yaɗa labaran Falasɗinawa ta wallafa ya nuna yadda sojojin Isra'ila ke kutsawa cikin sansanin 'yan gudun hijira na Jenin da ke Gaɓr Yamma da Kogin Jordan da ke ƙarƙashin mamaye.
Akwai kuma rahotannin wasu hare-hare a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan, kamar garuruwan Silwad da Nablus.
An kama aƙalla mutum goma, ciki har da wani yaro ɗan shekara 12 a Silwad, inji rahoton Wafa.
Kafofin yaɗa labaran Majalisar Dinkin Duniya da na Isra’ila sun ce ƙungiyoyin Falasdinawa na ci gaba da harba makaman roka a Isra’ila.
-
Rikicin kama-wuri-zauna ya haddasa fargaba a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan
-
'Ina takaicin yadda na gaza ceto rayuwar yaran da ke mutuwa a Gaza'