Sassan Zirin Gaza a safiyar yau
Wakilin BBC Rushdi Abualouf, wanda ke zaune a Gaza, ya aiko mana da wannan bidiyo da ke nuna hare-haren jiragen yakin Isra'ila suka yi matukar rugurguza gine-gine a Zirin.
Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya
A'isha Babangida, Mukhtar Adamu Bawa, Abdullahi Bello Diginza and Haruna Kakangi
Wakilin BBC Rushdi Abualouf, wanda ke zaune a Gaza, ya aiko mana da wannan bidiyo da ke nuna hare-haren jiragen yakin Isra'ila suka yi matukar rugurguza gine-gine a Zirin.
BBC ta kare shawarar da ta yanke cewa ba za ta kira 'yan ta-da-ƙayar-baya na Hamas da sunan ''yan ta'adda' ba, a cikin rahotannin da take yaɗawa game da hare-haren baya-bayan nan a Isra'ila.
Wani mai magana da yawun BBC ya ankarar da cewa akwai daɗaɗɗen matsayi da tashar labaran ta duniya ta ɗauka cewa masu aika rahotanninta, ba za su yi amfani da sunan 'yan ta'adda ba, su a kan kansu, sai dai fa idan suna ruwaito zancen wani.
Wani daɗaɗɗen wakilin BBC kan harkokin waje, John Simpson ya ce "kiran wani da sunan ɗan ta'adda, na nuna cewa, kana goyon bayan wani ɓangare ne a cikin lamari".
Sakataren tsaron Birtaniya Grant Shapps ya ce wannan manufa na "daf da zubar da mutuncin", tashar kuma akwai buƙatar BBC ta gano inda ta ajiye "tunaninta na sanin ya kamata".
Mai magana da yawun BBC na cewa: "BBC tashar labarai ce mai zaman kanta ta fuskar tsarin gabatar da aikin jarida, wadda aikinta shi ne ta bayyana haƙiƙanin abin da ke faruwa 'a ƙasa' ta yadda masu bibiyarmu za su iya yanke hukunci da kansu."
Ga sabbin bayanan da aka samu daga sojojin Isra'ila
Wani sabon labari daga rundunar sojojin Isra'ila - ta hannun mai magana da yawun rundunar Jonathan Conricus shi ne 'yan ta-da-kayar-baya na Hamas sun fille kawunan jarirai a lokacin da suka kai miyagun hare-hare a karshen mako.
Conricus ya ce wani mai binciken sanadin mutuwa da ya kai ziyara bayan kisan kiyashin da aka yi a Kibbutz Be'eriya ga gawawwakin kananan yara kuma ya tabbatar da yadda suka mutu.
"Na amsa cewa, abu ne da ya dauke mu tsawon lokaci kafin mu iya ainihin fahimta, kuma mu rarrabe wannan rahoto, amma dai yana da wuya a yarda cewa hatta Hamas tana iya aikata irin wannan aika-aika ta kidahumanci," ya ce.
"Ina jin yanzu muna iya cewa, da kwarin gwiwa, wannan ne abin da Hamas ta aikata...akwai gawawwaki warwatse a ko'ina, an gididdiba su."
An daure matar tsohon shugaban kasar Gabon Ali Bongo Odimba a gidan yari, kamar yadda lauyanta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Ana zargin Sylvia Bongo ne da laifin wawure dukiyar jama'a.
An hamɓarar da gwamnatin mijinta ranar 30 ga watan Agusta.
Lauya Francois Zimeray ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa daurin da aka yi mata a ranar Laraba "ba bisa ka'ida ba ne."
A watan jiya ne, aka tuhumi Sylvia Bongo da laifin halasta kuɗaɗen haram da kuma karbar kadarorin sata da kuma damfara.
An kuma tuhumi danta Noureddin Bongo Valentin da laifin almundahana, sannan an tsare shi kafin a yi masa shari'a.
Sojoji dai sun kwace mulkin kasar ne jim kadan bayan ayyana Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a Gabon.
Kungiyar ba da agaji a duniya ta Red Cross (ICRC) ta yi gargadin cewa asibitoci a Gaza na neman zama ɗakunan ajiye gawawwaki.
Tashar wutar lantarki daya tilo a Zirin Gaza ta daina aiki a ranar Laraba saboda karancin man fetur. Hakan na nufin Gaza - ciki har da asibitoci - za su koma dogaro da janareta, wanda kuma ke buƙatar karin man fetur a kai a kai.
Galibin wutar lantarkin da ake samu a Gaza, na fitowa ne daga Isra'ila, wadda ta katse wutar da yankin ke amfani da ita, bayan harin Hamas.
Daraktan Gabas ta Tsakiya a kungiyar Red Kuros, Fabrizio Carboni ya ce "Bacin ran dan'adam da wannan tashin hankali ya haifar, abu ne mai ban tsoro, kuma ina rokon bangarorin biyu su rage radadin da fararen hula ke fuskanta."
"Kamar yadda Gaza ta yi asarar wutar lantarki, ayyuka sun fi karfin asibitoci, suna sanya jarirai a cikin kwalaben ajiye bakwainin jarirai.yayin marasa lafiya tsofaffi ke bukatar na'urorin taimaka wa numfashi, haka ba sa iya daukar hotunan X-ray, "in ji shi.
Carboni ya kuma bayyana fargaba a kan Isra'ilawan da mayakan Hamas suka yi garkuwa da su - yana mai kira a gaggauta sakin su.
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa yara mata miliyan 7.6 a Najeriya, mafiya yawa daga yankunan arewacin kasar, ba sa samun damar karatu.
Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Cristian Munduate ce ta bayyana hakan a gidan gwamnatin Kano yayin bikin tunawa da ranar yara mata ta duniya ta shekarar 2023 da aka yi wa taken: “Lokacinmu ne yanzu – hakkinmu, makomarmu.”
Ta ce, “Yayin da nasarorin da ‘yan mata ke samu ke bayar da kwarin gwiwa ga sauran mata a wasu sassan duniya, yara mata miliyan 7.6 a Nijeriya, mafi yawa daga yankunan arewa ba sa samun wannan dama ta karatu."
“Abin ban tsoro shi ne, Najeriya na da kashi 15 cikin 100 na yaran da ba sa zuwa makaranta a duk duniya. Amma duk da haka, kashi 9 cikin 100 na matalautan mata ne ke da damar zuwa makarantar sakandare. Wannan ba ƙididdiga ba ce kawai, kira ne na a tashi tsaye."
"Amma ko yaya, a cikin waɗannan ƙalubalen, muna samun karin kwarin gwiwa a yau da gobe."
Ta kara da cewa, a yayin da Kano ke matsayi na biyu a jerin ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, lamarin da ya nuna akwai tsananin banbance-banbance wajen samun ilimi, akwai bukatar a kara jaddada canjin wajen samar da ilimi.
Kungiyar Hamas ta Falasɗinawa ta ce ta sako wata ‘yar Isra’ila da ‘ya’yanta biyu da take tsare da su, tun bayan hare-haren da ta kai ranar Asabar a cikin Isra’ila.
Har yanzu ba a tabbatar da sanarwar da dakarun na rundunar Qassam ta Hamas suka fitar ba, kuma wasu kafofin yaɗa labaran Isra'ila sun yi watsi da sanarwar, suna cewa da ma can ba a yi garkuwa da matar ba.
Tashar talbijin ta Aljazeera da ke Qatar ta yada wani bidiyo da ta ce yana nuna sakin matar da 'ya'yanta ne.
A bidiyon, an ga wata mata tana tattara kayanta da na ƴaƴanta a filin Allah ta'ala, daidai kusa da wata katanga, ga kuma wasu mayaƙa biyu dauke da makamai suna mata rakiya.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Isra'ila don nuna goyon bayan Amurka bayan harin Hamas
A cikin gajeriyar ziyarar tasa Blinken zai gana da jami'an Isra'ila da kuma shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas.
Ana sa ran Blinken zai nemi a sako mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su, wadanda wasunsu Amurkawa ne.
Zai kuma buƙaci a tsaigata wuta tare da neman hanyar tsira ga fararen hular Gaza gabanin yiwuwar kai hari daga Isra'ila.
Shugaban Falasɗinawan dai yana zaune ne a Yammacin Kogin Jordan, kuma abokin hamayyar siyasa ne ga Hamas a zirin Gaza.
Kafofin watsa labaran Rasha sun ce shugaba Putin ya isa Kyrgyzstan, a ziyararsa ta farko a zuwa wata kasa tun bayan da kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta bayar da sammacin kama shi.
A watan Maris ne aka ba da umarnin, saboda zarginsa da kwashe yara daga Ukraine zuwa Moscow, bayan kaddamar da yaƙi.
Putin zai gana da shugaban Kyrgyzstan, Sadyr Japarov, ya kuma halarci taron kasashen tsohor tarayyar Sobiyat.
Kyrgyzstan babbar kawar Rasha ce, amma bata amince da kotun hukunta manyan lafukan ta duniya ba.
Ga abubuwan da suka faru cikin sa'o'i kalilan da suka wuce a rikicin Isra'ila da Gaza:
Kenya ta ce za ta kawo karshen yarjejeniyar shekaru shida da ta bai wa likitocin Cuba fiye da 100 damar yin aiki a asibitocin ƙasar.
Ministar lafiya Susan Nakhumicha ta fada a ranar Laraba cewa matakin zai taimaka wajen magance ƙalubalen da ma’aikatan kiwon lafiyar Kenya ke fuskanta ciki har da rashin samun ayyukan yi.
“Mun yanke shawarar ba za mu sabunta yarjejeniyarmu da likitocin Cuba ba. Su kansu kwararrun likitocin mu sun himmatu wajen tabbatar da hakan,” in ji ta.
Yarjejeniyar shekarar 2017 ta kafa wani shiri na musanya wanda likitocin Cuba za su taimaka wajen cike giɓin da ake samu a asibitocin gundumomi yayin da 'yan Kenya kuma za su je Cuba don samun horar likitoci na musamman.
Har ila yau, akwai fargabar cewa gwamnatin Kenya na biyan kwararrun likitocin Cuba fiye da likitocin ƙasar duk da cewa wasu likitocin da aka horar a cikin gida ba su da aikin yi.
Likitoci da sauran ma’aikatan lafiya dai a ƙasar Kenya sun sha yajin aiki domin neman ƙarin albashi, da kyautata yanayin aiki da kuma ƙarin likitoci.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani mayaƙi na Hamas sunansa "mataccen mutum," bayan taron farko na sabuwar gwamnatin gaggawa ta kasar.
Netanyahu da ɗan adawa Benny Gantz - tsohon hafsan soji - sun haɗa gwamnatin haɗaka domin tunkarar yaƙi a ranar Laraba, inda suka ajiye adawarsu ta siyasa.
Gantz ya ce lokaci ne na yaƙi kuma sabuwar gwamnatin da aka kafa a shirye take ta "shafe Hamas daga doron kasa".
Majalisar Dinkin Duniya ta ce an tilastawa mutane dubu dari uku da arba'in a Gaza barin gidajensu yayin da Isra'ila ke ci gaba da luguden wuta a yankin a matsayin martani ga harin da Hamas ta kai a ranar Asabar.
Ma'aikatar lafiya ta Falasɗinawa ta ce hare-haren bama-bamai a yanzu sun kashe sama da mutane dubu ɗaya da dari biyu, da raunata sama da dubu biyar.
Da yake babu shiga ba fita, don haka babu damar kai kayan agaji.
Falaɗinawa dai suna kira da a samar da wata mashiga don kai kayan agaji da suka haɗa da kayan abinci da magunguna da man fetur.
Wani jami'in Masar ya ce kasar na kokarin tattaunawa da Isra'ila don ba da wannan dama.
Masu bibiyar mu barkanmu da safiyar Alhamis.
Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa tare da ni Aisha Babangida.
Ku kasance da mu tsawon yinin yau, domin sanin abubuwan da ke faruwa a sassan duniya daban-daban har ma da Najeriya.