Masu kare hakkin dan'adam sun koka a kan azabtar da mutane a kasar Masar
Kungiyoyin kare hakkin dan'adam sun ce amfani da azabtarwa da mahukuntan Masar ke yi, ya zama ruwan dare.
A cikin wani rahoto da aka mika wa kwamitin Majalisar Dinkin Duniya kan azabtarwa, bakin wasu kungiyoyin kare fararen hula shida ya zo daya, a kan cewa jami'an tsaron Masar na amfani da wasu hanyoyin azabtarwa da suka hada da duka da lalata da kuma amfani da lantarki don rufe bakin 'yan adawa.
Sabon shugaban kwamitin kula da harkokin waje na majalisar dattawan Amurka, Ben Cardin, ya yi barazanar dakatar da tallafin da Amurkar ke bai wa Masa, matukar gwamnatin birnin Alkahira ba ta canza hali ba.
Ana zargin shugaba Abdel Fattah al-Sisi da murkushe 'yan adawa a tsawon shekara goman da ya kwashe yana mulki.