Gane Mini Hanya: Rawar da matasa za su taka a fagen mulki
Burin kowace al`umma shi ne ta gina matasa a fannoni daban-daban na rayuwa domin su kasance manyan gobe.
Sai dai a fannin mulki, musamman a kasashen nahiyar Afirka, ciki har da Najeriya, za a iya cewa an samu akasi.
Shin me ke yin cikas ga matasa a harkar siyasa, kuma ta wace hanya za a shawo kan matsalar?
A filinmu na Gane Mini Hanya na wannan makon, Ibrahim Isa ya tattauna da Farfesa Jibrin Ibrahimy, masanin harkokin siyasa a shiyyar Afirka ta yamma.
Shehin malamin ya fara ne da bayani a kan fa`idar shigar da matasa a cikin harkar mulki