Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Majalisa ba ta tabbatar da El-Rufai a matsayin minista ba

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Rabiatu Kabir Runka, Ahmad Tijjani Bawage and Badamasi Abdulkadir Mukhtar

  1. Faransa ta dakatar da duk wani tallafi da ta ke bai wa Burkina Faso

    Faransa ta sanar da dakatar da duk wani tallafi da ta ke bai wa Burkina Faso da suka haɗa da ayyukan ci gaban ƙasa da kasafin kuɗi.

    Sanarwar na zuwa ne bayan gwamnatin sojin Burkina Faso ta ce za ta ɗauki duk wani matakin soji da ake son ɗauka kan jagororin juyin mulki a Nijar, a matsayin ƙaddamar da yaƙi gare su.

    Ita ma gwamnatin sojin Mali ta ɗauki irin wannan matakin, da jaddada goyon baya ga sojojin makofciyarsu wato Nijar.

  2. An dawo hutun rabin lokaci a wasan Ingila da Najeriya

    Ƴan wasan Ingila da kuma Super Falcons ta Najeriya sun shiga fili , inda za a ci gaba da fafatawa.

    Yanzu saura mintuna 45 kafin sanin kungiyar da za ta yi nasara.

    Shin Ingila ce ko Najeriya? lokaci kaɗai zai nuna.

  3. An tafi hutun rabin lokaci babu ci tsakanin Ingila da Najeriya

    An tafi hutun rabin lokaci a wasan da Najeriya take buga wa da Ingila a gasar cin kofin duniya ta mata.

    Sai dai Super Falcons ce ta fi buga kwallo kafin a tafi hutun rabin lokaci, inda ta kai hare-hare sau tara a ragar Ingila.

    Duk kungiyar da ta samu nasara ita ce za ta kai zagayen quarter finals.

  4. Nijar ta sanar da rufe sararin samaniyarta da iyakokin ƙasar

    A jamhuriyar Nijar, wa'adin da ƙungiyar ECOWAS ta bai wa sojojin da sukai juyin mulki a Jamhuriyar Nijar na su koma barikokinsu da maida mulki ga farar hula ko su ɗauki matakin soji, ya cika ba tare da sun bi umarnin ba.

    Gwamnatin sojin Nijar ta sanar da rufe sararin samaniyar ƙasar, da kuma shirin kare iyakokin ƙasar na kasa. Wakiliyar BBC ta ce "Mun sa ran kungiyar Ecowas za ta fitar da wata sanarwa daidai lokacin da wa'adin ya cika, ko matakin da za ta dauka nan gaba, amma shiru ka ke ji."

    Kawunan mambobin ƙungiyar ECOWAS ya rarrabu kan ɗaukar matakin sojin, inda Nigeria da Ivory Coast suka kafe kan lallai a dawo da mulki hannun shugaba Muhammad Bazoum, su kuwa Mali da Burkina Faso ke goyon bayan sojojin da sukai juyin mulkin.

  5. Super Falcons na karawa da Ingila a gasar cin kofin duniya ta mata

    Kungiyar kwallon kafar mata ta Najeriya na karawa da Ingila a gasar cin Kofin duniya ta mata a zagaye na biyu da ƙasashen Australiya da Newzealand ke karɓar bakunci.

    Super Falcons ta kawo wannan mataki ne bayan karewa a mataki na biyu a rukuninsu.

    Suna kuma da yar wasan gaba Asisat Oshoala wadda ke ganiyarta a fagen tamaula a yanzu.

    Duk da cewa ana hasashen cewa Ingila za ta iya samun nasara, amma komai na iya faruwa ganin irin zaƙakuran ƴan wasa da Najeriya ke da shi.

  6. Buɗewa

    Masu bibiyar mu a shafin BBC Hausa barkan mu da safiyar Litinin- Mande tushen aiki.

    Rabiatu Kabir Runka ce ke fatan kasancewa tare da ku.

    Ku kasance da mu domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwaɓtanta da kuma sauran sassan duniya.