Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Nan da shekara ɗaya, za a samu kyakkyawan sauyi a Najeriya - Shettima

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan dake faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Makamai masu linzami sun lalata gine-gine a Dnipro

    Wasu makamai masu linzami da aka harba sun faɗa kan wasu gine-gine biyu da ke tsakiyar gabashin birnin Dnipro na Ukraine.

    Wata tawagar BBC da ke birnin ta ce hare-haren sun lalata wani gini a birnin, sannan wani gini na jami'an tsaro wanda ba a amfani da shi ya rushe.

    An ga yadda gilasai suka farfashe suka warwatsu kan titunan da ke kusa da gine-ginen da makaman suka faɗa.

    mutane da dama ne suka samu raunuka, to amma babu rahoton rasa rai kawo yanzu.

  2. Ni ne ɗan takarar da zan lashe zaɓe mai zuwa -Trump

    Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya ce yana ganin shi kaɗai ne ɗan takarar da zai iya lashe zaɓen shugaban ƙasar da ke tafe.

    Yayin da yake jawabin ga taron gangamin magoya bayan jam’iyyarsa ta Republican, Mista Trump ya ce wannan ne dalilin da ya sa yake fuskantar tuhume-tuhume a kan aikata ba daidai ba.

    Mista Trump shi ne ɗan takara na 13 da jam’iyyar Republican ta tsayar da zai yi jawabi ga taron magoya bayanta.

    Taron gangamin ya kuma yi wa wani ɗan takarar daga jihar Texas kuwa ihu, bayan da ya ce Trump na son sake tsayawa takara ne saboda kada a kai shi gidan yari.

    Tuni masu shigar da ƙara na gwamnatin ƙasar suka ƙara faɗaɗa binciken da ake yi wa Mista Trump kan riƙe wasu muhimman takardun gwamnati bayan ya sauka daga mulki.

  3. Sallama

    Masu bin mu a wannan shafi barkan mu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kuna iya lekawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.