Habasha ta mayar da martani ga rahoton BBC kan takardun haihuwan 'yan gudun hijira

Asalin hoton, bbc
Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Habasha (RRS) ta mayar da martani ga rahoton BBC a makon da ya gabata cewa ba a bayar da takardar shaidar haihuwa ga jariran da iyaye ‘yan gudun hijirar Eritiriya suka haifa ba.
Iyayen sun ce hakan na kawo cikas ga haduwar iyali.
RRS ta kira ikirarin cewa "zargin ba shi da tushe"
A cikin wata sanarwa da ta fitar, ta ce "ana yin rajista tun watan Nuwamba 2022 kuma an yi wa yara 'yan Eritrea 2,149 rajista.
Sai dai sanarwar ba ta yi magana kan ko an bayar da takardar shaidar haihuwa da iyalai ke bukata ba ko a'a.
Wani mutum da ke zaune a Jamus ya shaida wa BBC cewa ya dade yana jiran ya kawo matarsa da 'ya'yansa su zauna da shi amma ofishin jakadancin Jamus na buƙatar takardun haihuwa kafin ya ba da bizar ga jariran.
"Na ga amsa daga RRS. Matsalarmu ba rajista ba ce – abin da muke bukata shi ne takardar shaidar haihuwa wadda ofishin jakadancin Jamus ke nema,” in ji wani uba.
Wani kuma ya ce: “Matanmu sun kwashe watanni suna zuwa ofisoshin RRS suna neman takardar shaidar haihuwa amma duk da haka har yanzu muna jira duk da alkawuran da aka sha yi mana.”




















