An gabatar da ƙudurin ƙara albashin Tinubu da sauran shugabanni

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran dake faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida and Haruna Kakangi

  1. 'Yan Isra'ila sun ci gaba da kai harin maida martani bayan harbe-harbe da aka yi

    ...

    Asalin hoton, EPA

    An harbe wani Bafalasdine har lahira tare da raunata wasu da dama bayan da wasu 'yan Isra'ila mazauna yankin suka kai wani mummunan hari a yammacin gabar kogin Jordan da isra'ila ta mamaye.

    Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa suna fargabar tsira rayukansu yayin da daruruwan 'yan isra'ila dauke da makamai suka kona gidaje da motoci a garin Turmusaya.

    Daya daga cikin mutanen ya zargi sojojin Isra'ila da barin su ba tare da taimako ba na tsawon mintuna 45 yayin harin.

    “Sun bai wa mazauna yankin damar yin hakan,” in ji shi.

    Ana ganin cewa harin ramuwar gayya ne, ganin ya zo sa'o'i bayan jana'izar wani matashi dan shekaru 17 da haihuwa wanda ke cikin wasu 'yan Isra'ila hudu da wasu 'yan bindiga Falasdinawan suka harbe a wani gidan mai a ranar Talata.

    Sojojin Isra'ila sun yi Allah wadai da harin da mazaunan suka kai, amma ba su amsa tambayoyi kan saurin da suka yi na kai agaji ko kuma yanayin matakin da suka dauka ba.

    Ana ci gaba da fargabar barkewar wani mummunan tashin hankali a yammacin gabar kogin Jordan, bayan wani farmaki da sojojin Isra'ila suka kai a birnin Jenin a ranar Litinin da ta gabata, inda suka kashe Falasdinawa bakwai.

  2. A yi wa tsofaffi adalci a Najeriya - 'Yan fafutuka

    ...

    Darakta Janar na Cibiyar kula da tsofoffi ta kasa (NSCC), Dokta Emem Omokaro, ya bukaci masu ruwa da tsaki da su karfafa hanyoyin da tsare-tsare don tabbatar da adalci ga tsofaffi a kasar nan.

    Omokaro, ya yi wannan kiran a ranar Larabar da ta gabata a Abuja, yayin wani taron masu ruwa da tsaki, ya yi kira da a hada kai don tabbatar da adalci ga tsofaffi.

    Taron masu ruwa da tsaki da aka yi wa lakabi da ‘Elder Justice’, cibiyar ce ta shirya tare da hadin gwiwar hukumar kare hakkokin Dan Adam ta kasa da kuma Majalisar bada agaji ta Shari’a.

    Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, an shirya taron ne a matsayin wani bangare na gudanar da bikin ranar wayar da kan dattijai ta duniya

    Ranar ta na goyan bayan Shirin Majalisar Dinkin Duniya wanda ya yarda Muhimmancin cin zarafin dattijai a matsayin batun lafiyar jama'a ce da kuma tauye hakkin dan adam, kuma ana kokarin wayar da kan mutane. da kungiyoyi da al'ummomi game da cin zarafi, sakaci da cin gajiyar dattawa.

    A cewarta, "Martanin mu a nan shi ne ta yaya za mu tabbatar da adalci ga tsofaffi, kuma babban jawabi na zai kasance a kan hadin gwiwa a kan shari'ar dattijai, da kuma inganta tsarin da ke ba da damar yin adalci ga tsofaffi ta hanyar aiki tare.

    A nasa jawabin, Sakataren zartarwa, na hukumar kare hakkin dan adam (NHRC), Mista Tony Ojukwu, wanda Misis Fidelia Oroh ta wakilta, ya bayyana bukatar hadin gwiwa don dakile cin zarafin tsofaffi a Najeriya.

  3. Fiye da mutane 20 sun jikkata bayan fashewar wani abu a Paris

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Mutane 29 ne suka jikkata, hudu daga cikinsu sun ji munanan raunuka, bayan fashewar wani abu a tsakiyar birnin Paris.

    Fashewar ta faru ne a wani gini da ke dauke da makarantar zane da kuma babban ofishin ilimin Katolika da ke Rue Saint-Jacques, a yanki na biyar na babban birnin Faransa.

    Ma’aikatan agajin gaggawa na binciken tarkacen ginin, inda ake tunanin akalla mutane biyu ba su bayyana ba..

    A cewar shaidu, an ji warin iskar gas kafin fashewar.

    Mai gabatar da kara na birnin Paris, Laure Beccuau, bayan isa wurin da lamarin ya faru, ta ce bidiyon kyamara ya nuna cewa fashewar ta faru ne a cikin ginin da ke kusa da cocin Val de Grace, in ji jaridar Le Parisien.

    Sai dai hukumomin kasar sun ce kawo yanzu ba a tantance musabbabin fashewar ba.

    Da farko dai wuta ta mamaye ginin, amma daga baya an shawo kan gobarar, in ji shugaban 'yan sandan Paris Laurent Nunez.

    ,,,

    Asalin hoton, Reuters

  4. Kamaru ta dakatar da ziyarar jakadan Faransa mai rajin kare ƴan luwaɗi da maɗigo

    Shugaban Kamaru, Paul Biya

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Shugaban Kamaru, Paul Biya

    Ministan harkokin wajen Kamaru, Lejeune Mbella ya ce gwamnati ba ta amince da ziyarar da jami'in diflomasiyyar Faransa zai kai ƙasar ba, don tattaunawa a kan al'amuran da suka shafi 'yancin masu luwaɗi da maɗigo a Kamaru.

    Ya ce hakan ya faru ne saboda luwaɗi "laifi ne a idon dokar Kamaru.

    Jakadan Faransa mai kula da ‘yancin ‘yan luwaɗi da maɗigo, Jean-Marc Berthon, ya so kai ziyara Kamaru ne daga ranar 27 ga watan Yuni zuwa 1 ga watan Yuli domin tattaunawa da hukumomi kan kare ‘yancin masu neman jinsi ɗaya.

    Ziyarar da Mista Berthon ya so kai wa ta zo ne a daidai lokacin da hukumar sadarwa ta Kamaru ta gargaɗi kafafen yada labarai a kan tallata harkokin da shafi 'yan luwaɗi da maɗigo.

    Ana taƙaita 'yancin ƴan luwaɗi da maɗigo a yawancin ƙasashen Afirka, wasu ƙasashe na suna tsaurara dokoki kan rukunin al'ummar.

    A shekara ta 2021, ƙungiyar kare haƙƙin ɗan'adam ta yi tir da tsangwamar da ake yi wa ƴan luwaɗi da maɗigo a Kamaru.

  5. An kai hare-haren kunar bakin wake a Somaliya yayin da AU ke yunkurin rage sojoji

    ...

    Kungiyar al-Shabab ta Somaliya ta ce ta kai hare-haren kunar bakin wake guda biyu a kan cibiyoyin soji.

    Wasu rahotanni sun ce mutane da dama ne suka mutu sakamakon fashewar wasu abubuwa a wajen wani sansanin soji da ke kudu maso yammacin garin Bardere inda aka girke sojojin Somaliya da na Habasha.

    Harin dai na zuwa ne sa'o'i kadan bayan kungiyar Tarayyar Afirka ta ce za ta rage yawan sojojin da take turawa a Somalia.

  6. Gambia za ta gwada magungunan Indiya bayan badakalar maganin tari

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Daya daga cikin ‘ya’yan wannan mutumin ta mutu a kasar Gambia a watan Satumban da ya gabata bayan ta sha wani maganin tari da aka yi a kasar Indiya

    Gambia tana aiwatar da bincike na dole da gwajin duk magungunan da aka shigo da su daga Indiya.

    Sabbin matakan dai na zuwa ne bayan da akalla yara 70 suka mutu a kasar a bara bayan shan maganin tari da aka yi a Indiya.

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce an gurbata su da sinadarai masu guba da aka saba amfani da su a cikin ruwan birki na mota da sauran kayayyakin masana'antu.

    Daga baya Indiya ta cean tantance magungunan a lokacin da aka gwada su a gida, amma WHO ta amsa cewa ta tsaya kan fadakarwar da aka bayar kan maganin tari guda hudu.

    Daga baya an danganta wasu rukunen magungunan da mutuwar yara 19 a Uzbekistan.

    Indiya, wacce masana'antun ta ke harhada kashi daya cikin uku na magungunan duniya, ita ma ta wajabta wa masu sarrafa maganin tari daga ranar 1 ga watan Yuni su yi gwajin samfurin magungunan kafin fitar da kayayyakinsu.

    Gambiya na duba yiwuwar daukar matakin shari'a saboda mutanen da suka mutu.

  7. Ɗaya daga cikin masu sanya mutane azumin mutuwa a Kenya, ya mutu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Daya daga cikin mutane 30 da ke hannun ‘yan sanda bisa zargin kasancewa mambobin wata ƙungiyar asiri da ke horo da yunwa a Kenya, ya mutu.

    Joseph Juma Buyuka - tare da wasu a cikin waɗanda ake zargi - sun yi yajin cin abinci a farkon wannan wata don nuna adawa game da kama shin da aka yi.

    An garzaya da shi zuwa asibiti a garin Malindi da ke kudu maso gabashin Kenya, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

    “Muna zargin ya mutu ne sanadin larurorin ƙauracewa abinci. Za mu iya jira a yi gwajin gawa don gano ainihin musabbabin mutuwar,” wani babban mai shigar da ƙara ya faɗa wa wata kotu a Mombasa, babban garin gabar tekun Kenya.

    Har yanzu, babu ɗaya a cikin wadanda ake zargi, waɗanda suka haɗar da shugaban ƙungiyar asiri, Paul Nthenge Mackenzie da aka gurfanar a kotu, yayin da ‘yan sanda ke ci gaba da bincike.

    An yi imanin cewa faston da sauran waɗanda ake zargin sun ingiza mambobin Cocin Good News International wajen kashe kansu da yunwa.

    Tun a watan Afrilu, aka tono gawawwakin mutane 336 daga kaburbura marasa zurfi a wani dajin da ke nesa.

    Fiye da wasu 600 ne suka bace.

    An kwantar da mutum biyu da ake tsare da su saboda su ma suna yajin cin abinci, a asibiti cikin mawuyacin hali.

    Kotun za ta yanke hukunci a ranar Talata mai zuwa ko Mista Mackenzie zai ci gaba da kasancewa a hannun ‘yan sanda tsawon kwana 60 ko a'a.

  8. An gabatar da ƙudurin ƙara albashin Tinubu da sauran shugabanni

    Nigerian President

    Asalin hoton, Tinubu/Facebook

    Hukumar tattarawa da raba kuɗaɗen shiga a Najeriya ta amince da ƙudurin ƙarin albashin zaɓaɓɓun 'yan siyasa ciki har da shugaban ƙasa da mataimakinsa.

    Ƙudurin zai kuma shafi gwamnoni da mataimakansu da 'yan majalisa da alƙalai da sauran masu riƙe da muƙaman gwamnati.

    Ta ce ƙarin wanda aka yi a kan tsagwaron albashi (ban da alawus-alawus) ya kai kashi 114, abin da ke nufin shugaban ƙasa zai iya karɓar albashin da ya kusan kai naira miliyan biyu duk wata.

    Shugaban hukumar (RMAFC) Muhammadu Shehu ya faɗa wa BBC cewa sun yi nazari bisa la'akari da halin da ake ciki a ƙasa, kafin yin ƙarin albashin.

    Sai dai a cewarsa, matakin ƙuduri ne kawai don kuwa sai an gabatar wa Majalisar Tarayya don amincewa kafin ya zama doka.

    Haka zalika ƙarin zai shafi ministoci da kwamishinoni da mataimaka na musamman kamar yadda sashe na 84 da sashe na 124 na tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

    A cewar hukumar, karon ƙarshe da aka yi wa zaɓaɓɓun 'yan siyasar ƙarin albashi a Najeriya, shi ne shekara ta 2007.

  9. Saƙon wata mai ciwon sikila ga al'umma

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  10. Ɗan wasan Ghana Asamoah Gyan ya yi ritaya

    Asamoah Gyan

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Asamoah Gyan

    Tauraron dan kwallon Ghana Asamoah Gyan ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon ƙafa.

    A wani saƙon tuwita, Gyan ya ce "Lokaci ya yi da za a rataye riga da takalma yayin da na yi ritaya daga wasan kwallon kafa."

    Dan wasan na gaba ya ci kwallaye 51 a wasanni 109 da ya buga wa ƙasar, abin da ya sa ya zama dan wasan da ya fi cin kwallaye a tarihin Ghana.

    Dan wasan mai shekaru 37, ya fara buga wasa a matakin ƙungiya ne a shekara ta 2003, inda ya buga wasa a kungiyar farko ta Ghana, Liberty Professionals, sannan ya buga wasa a Turai a Udinese ta Italiya da Rennes na Faransa da kuma Sunderland ta Premier ta Ingila.

    Ya taba buga wasa a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, a kungiyar Al Ain, ya kuma taimaka wa ƙungiyar ta lashe kofin babbar gasar ƙasar ta Pro-League sannan kuma ya zama dan wasan da ya fi cin kwallaye inda ya zura kwallaye 28 a wasanni 32.

    A Ghana, Gyan ya yi fice a babbar tawagar kasar, Black Stars, a gasar cin kofin duniya ta Fifa guda uku - a 2006, 2010 da 2014.

    Shi ne dan wasan da ya fi cin kwallaye a gasar cin kofin duniya a Afirka, inda ya ci kwallaye shida.

    Ya buga wa ƙasarsa wasanni bakwai na gasar cin kofin nahiyar Afirka, inda Black Stars ta ƙare a matsayi na uku a shekara ta 2008 sannan a matsayi na biyu a 2010 da 2015.

  11. Mali ta zargi dakarun Majalisar Ɗinkin Duniya da leƙen asiri

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin mulkin soji ta Mali ta shigar da ƙara kan rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a ƙasar kan wani rahoto da ya zargi sojojin Mali da kawayensu da kisan daruruwan mutane a bara.

    Ƙarar ta ce rundunar, Minusma, ta yi amfani da tauraron ɗan'adam wajen tattara bayanai ba tare da izinin gwamnati ba.

    Hakan ya kasance "leken asiri" kuma ya kamata a yi bincike, in ji ofishin mai shigar da ƙara na ƙasar Mali.

    Ya kuma bayyana jami’an rundunar a matsayin masu hannu wajen aikata laifuka, na leken asiri, raunana wa sojoji gwiwa, da yin amfani da takardun karya da kuma cutar da tsaron kasar”.

    Wani rahoto da babban kwamishinan kare haƙƙin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar ya zargi sojojin ƙasar Mali da "jami'an tsaron ƙasashen waje" da kashe sama da mutane 500 a wani farmaki da aka kai a kauyen Moura da ke tsakiyar ƙasar Mali a watan Maris din bara. Gwamnatocin Mali da Rasha duk sun yi tir da wannan rahoton.

    Wannan sabon ƙorafi na gwamnatin rikon kwarya ta Mali na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan ministan harkokin wajen ƙasar, Abdoulaye Diop ya yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da ta janye dakarunta na wanzar da zaman lafiya daga ƙasarsa "ba tare da bata lokaci ba".

    Wannan dai wani mataki ne na nuna adawa da shigar kasashen ketare cikin lamurran ƙasar, wadda sojoji ke jagoranta tun bayan da suka kwace mulki.

    Gwamnatin sojin na ci gaba da karfafa alaka da kungiyar sojojin haya na Wagner ta kasar Rasha.

  12. Gwamnati ta haramta yin acaɓa a birnin Calabar

    Acaɓa
    Bayanan hoto, ...

    Gwamnatin jihar Cross River ta bayar da umarnin haramta duk wasu ayyukan acaɓa a ƙwaryar babban birnin Calabar.

    Babban sakataren yada labarai na gwamnan, Emmanuel Ogbeche ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, inda ya bayyana cewa haramcin ya biyo bayan tattaunawa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar.

    A cewar sanarwar, an taƙaita ayyukan acaɓa ne a unguwannin gefe-gefen birnin ƙasar.

    Gwamnatin jihar ta yi gargadin cewa duk wanda aka kama yana karya dokar, za a ƙwace babur din tare da hukunta wanda ya aikata laifin.

    Gwamnatin jihar ta kuma yi gargadi a kan barnatar da dukiyoyin al’umma kamar fitulun kan hanya da masu bayar da hannu.

  13. Faɗa ya sake rincaɓewa a Khartoum

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Rahotanni daga Sudan na cewa ana gwabza fada a dukkan sassan babban birnin ƙasar, jim kaɗan kafin ƙarewar wa'adin tsagaita buɗe wuta na kwanaki uku, wanda ya cika da sanyin safiyar yau Laraba.

    Shaidu sun ce an gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun Rapid Support Forces (RSF) a birnin Khartoum.

    Akwai kuma rahotannin amfani da makaman kaɓo jiragen yaƙi a Omdurman.

    Saudiyya da Amurka ne suka shiga tsakanin domin tabbatar da tsagaita wutar na baya-bayan nan, sai dai kamar sauran lokutan baya an samu rahotannin karya yarjejeniyar.

    Rikicin tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF ya ɓarke ne a watan Afrilun bana.

  14. Wace nasara shugabannin Afirka suka cimma a ziyarar sasanta Ukraine da Rasha?

  15. Abba ya mayar da Muhuyi Magaji kan muƙaminsa

    Barr. Muhuyi

    Asalin hoton, FACEBOOK/MUHUYI MAGAJI RIMIN GADO

    Bayanan hoto, ...

    Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da mayar da Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado a matsayin Shugaban Hukumar Sauraron Korafe-korafen Al'umma da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta jihar Kano (PCACC), domin kammala wa’adinsa.

    Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban sakataren yada labaran gwamnan jihar ta Kano.

    Idan za a iya tunanwa, gwamnatin da ta gabata ta Abdullahi Umar Gnaduje ta dakatar da Muhuyi tare da tsige shi daga mukaminsa bayan majalisar dokokin jihar ta ce tana da shakku kan yadda yake gudanar da ayyukansa.

    Sanarwar ta bayyana cewa Barista Muhuyi zai koma kan aikinsa ne nan take.

  16. Kenya za ta zamanantar da makaman yakin sojinta

    t

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan tsaron kasar Kenya Aden Duale ya ce nan da watanni uku masu zuwa gwamnatin ƙasar za ta zamanantar da makaman sojin ƙasar, don dakile hare-hare da kungiyar al-Shabab da ke Somaliya mai makwabtaka ke kaiwa cikin kasar.

    A baya-bayan nan wani hari da mayaƙan suka kai gundumar Madera ya yi sanadiyyar mutuwar mutum uku ciki har da 'yan sanda biyu.

    Kimanin jami'an tsaro 22 ne aka kashe cikin makonni biyun da suka gabata sakamakon hare-haren 'yan bindiga a yankin Lamu da ke gabar teku da kuma gabashin Garissa da ke kan iyaka da Somaliya.

    "Daga cikin makaman har da masu gano abubuwan fashewa da aka dasa a ƙarƙashin ƙasa''.

    Ana ci gaba da shirye-shiryen sake bude kan iyakar kasashen biyu a hukumance, karon farko cikin shekaru goma, lokacin da sojojin Kenya suka fara kai farmaki kan kungiyar al-Qaeda da ke Somaliya.

    Yaƙin soji kan al-Shabab da sojojin Somaliya suka fara a watan Agustan da ya gabata ya janyo hasarar yankuna masu yawa ga kungiyar ta'addanci.

    Ana sa ran sojojin Kenya za su shiga kashi na biyu na wannan farmakin, lamarin da ya sa al-Shabab ta zafafa kai hare-hare a Kenya.

  17. Mutum 36 sun mutu a wani mummunan rikici a Somaliya

    Somalia
    Bayanan hoto, ...

    Akalla mutane 36 ne suka mutu a wasu tashe-tashen hankula a jihar Puntland da kuma yankin Lower Shabellebiyu da ke ƙasar Somaliya.

    Likitoci sun ce aƙalla mutum 26 ne suka mutu a wani kazamin fada da aka gwabza a ranar Talata a Garoowe, babban birnin jihar Puntland.

    Yayin da wasu 10 suka mutu bayan wasu bama-bamai da aka sarrafa daga nesa suka tashi a wani ƙauye kudu maso yammacin Mogadishu babban birnin Somalia.

    Shaidu sun ce mutane da dama ne suka mutu a fashewar bam na farko sannan bam na biyu ya tashi a lokacin da fararen hula da sojoji suka je wajen domin aikin ceto.

  18. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar mu a wannan shafi Aisha Babangida ce ke muku barka da safiya tare da fatan kasancewa da ku a wannan rana ta Laraba.

    Za mu kawo muku labarai da rahotanni iri-iri daga sassan duniya.

    Sai ku kasance da mu.